Home General Za a karɓe wa ƴan Najeriyar da aka samu da laifi a...

Za a karɓe wa ƴan Najeriyar da aka samu da laifi a waje fasfo na shekara 10

Majalisar dattawan Najeriya ta amince a haramta wa duk wani ɗan ƙasar da aka samu da aikata laifi a ƙasashen waje, yin amfani da fasfon Najeriya na tsawon shekara 10.

Majalisar ta amince da hakan ne a yayin zaman da ta yi a Abuja, a ranar Talata

Sanata Abubakar Bello mai wakiltar jihar Neja ta arewa ne ya gabatar da ƙudurin a gaban majalisar, a wani ɓangare na yi wa dokar fasfo ɗin garambawul.

Ƙudurin ya buƙaci a karɓe fasfo ɗin ne na tsawon shekara 10 mafi ƙaranci, abun da suke ganin zai taimaka wajen sanya ƴanƙasar da ke waje kuma suke aikata manyan laifuka shiga taitayinsu.

Ƴan majalisar na fatan matakin zai taimaka wajen magance ɓata sunan ƙasar da wasu ke yi a ƙasashen ƙetare.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp