Home Labarai Dalilin Tinubu na soke afuwar da Ya yiwa Maryam Sanda

Dalilin Tinubu na soke afuwar da Ya yiwa Maryam Sanda

 Jaridar The Punch ta ruwaito cewa bayan yawan suka da cece-kuce daga jama’a kan sahihancin afuwar, shugaban ƙasa ya soke cikakkiyar afuwar, tare da mayar da hukuncin zuwa daurin shekaru 12 a gidan yari.

A watan Afrilu 2020 ne kotu ta samu Maryam Sanda da laifin kashe mijinta, ɗan siyasa kuma ɗan gidan tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Haliru Bello, bayan muhawara ta cikin gida ta kai ga rikici.

A lokacin bikin ranar ‘yancin kai ta bana, an saka sunanta cikin jerin mutanen da shugaban ƙasa ya ba wa afuwa, lamarin da ya jawo matsanancin bacin rai daga jama’a, musamman daga kungiyoyin kare haƙƙin mata da iyalai.

Wata majiya daga fadar shugaban ƙasa ta tabbatar wa da manema labarai cewa an duba batun afuwar nan daga farko, kuma aka yanke shawarar a soke ta domin tabbatar da adalcinta ga waɗanda abin ya shafa.

Da wannan sabon mataki, Maryam Sanda za ta ci gaba da zaman gidan yari na shekaru 12, bisa umarnin da fadar shugaban ƙasa ta tabbatar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
ICPC za ta ci gaba da binciken shugaban NMDPRA duk da Dangote ya janye ƙorafinsaKu daina kirana da na janye takarar shugabancin kasa a shekarar 2027Ƴansanda sun ɗauke makeken bam ɗin da aka gani a jihar NejaSojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace a BornoNan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -TinubuAmurka ta fara kai harin soji Arewacin NijeriyaSojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a BornoGwamnatin Nijeriya ta yi watsi da kudirin hukuncin kisa ga masu garkuwaADC ta buƙaci a dakatar da aiwatar da sabuwar dokar harajiGwamnati Nijeriya ta haramta fitar da itace zuwa ƙasashen wajeTinubu ya maye gurbin Engr Farouk daga shugabancin hukumar NMDPRAICPC ta ce zata binciki shugaban hukumar NMDPRAZa mu ci gaba da kamen masu bakin gilashin mota - Yan sandaMajalisa ta amince da naɗin sabbin jakadun da Tinubu ya gabatarShugaban Najeriya zai iya dakatar da gwamna - Kotun Ƙoli
X whatsapp