Home Labarai Dalilin Tinubu na soke afuwar da Ya yiwa Maryam Sanda

Dalilin Tinubu na soke afuwar da Ya yiwa Maryam Sanda

 Jaridar The Punch ta ruwaito cewa bayan yawan suka da cece-kuce daga jama’a kan sahihancin afuwar, shugaban ƙasa ya soke cikakkiyar afuwar, tare da mayar da hukuncin zuwa daurin shekaru 12 a gidan yari.

A watan Afrilu 2020 ne kotu ta samu Maryam Sanda da laifin kashe mijinta, ɗan siyasa kuma ɗan gidan tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Haliru Bello, bayan muhawara ta cikin gida ta kai ga rikici.

A lokacin bikin ranar ‘yancin kai ta bana, an saka sunanta cikin jerin mutanen da shugaban ƙasa ya ba wa afuwa, lamarin da ya jawo matsanancin bacin rai daga jama’a, musamman daga kungiyoyin kare haƙƙin mata da iyalai.

Wata majiya daga fadar shugaban ƙasa ta tabbatar wa da manema labarai cewa an duba batun afuwar nan daga farko, kuma aka yanke shawarar a soke ta domin tabbatar da adalcinta ga waɗanda abin ya shafa.

Da wannan sabon mataki, Maryam Sanda za ta ci gaba da zaman gidan yari na shekaru 12, bisa umarnin da fadar shugaban ƙasa ta tabbatar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin MotaNNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar DeltaKotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Maryam SandaKotu ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige gidan yariHar yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso - TuggaNajeriya ta ce jirgin ta ya yi saukar gaggawa ne a Burkina FasoBurkina Faso ta tsare jirgin sojin Najeriya kan keta sararin samaniyar ƙasarKwankwaso ya ce matsalar tsaro na neman fin karfin Gwamnatin NijeriyaAn ceto wasu daga cikin daliban da aka sace a makarantar Papiri da ke jihar NejaAmnesty ba bukaci a gaggauta sakin Muhuyi MagajiAkwai sa hannun 'yan siyasa a kamen da aka yiwa Muhuyi - Gwamnatin KanoMajalisa ta amince da naɗin Chris Musa ministan tsaron NajeriyaWadanda aka sace a Cocin jihar Kwara sun shaki iskar 'yanciGwamnatin Nasarawa za ta kafa ƴan sandan JihaGwamnan Osun Ademola Adeleke ya fice daga jam’iyyar PDP
X whatsapp