Home Labarai Katu ta sami Nnamdi Kanu da laifukan ta’addanci

Katu ta sami Nnamdi Kanu da laifukan ta’addanci

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta samu jagoran ƙungiyar ƴan aware ta Biafra, Nnamdi Kanu da laifuka bakwai da ake tuhumar sa da aikatawa masu alaƙa da ta’addanci.

Alƙalain da yake shari’ar, Mai Shari’a James Omotosho ya ce masu gabatar da ƙarar sun tabbatar da tuhume-tuhumen da ake yi wa Nanamdi Kanu.

Tuhume-tuhumen da ake yi wa Kanu sun haɗa da ta’addanci da tunzura jama’a su kashe ƴan sanda da kasancewa mamba a haramtacciyar ƙungiyar IPOB da gwamnatin Najeriya ta haramta da kuma yaɗa farfagandar ta’addanci.

Mai Shari’a Omotosho ya ɗage zaman na wani ɗan lokaci inda ya ce zai yanke wa Nnamdi Kanu hukunci idan aka koma nan ba da jimawa ba.

Ana sa ran wannan ya kawo ƙarshen kimanin shekara 10 da aka kwashe ana shari’a, tun bayan da gwamnati ta gurfanar da shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp