Home General Kotu ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin daurin rai da rai

Kotu ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin daurin rai da rai

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin daurin rai da rai bisa samunsa da dukkan laifukan da ake tuhumarsa da su.

Kotun ta yanke masa hukuncin ne bayan samunsa da laifuka bakwai, waɗanda suke da alaƙa da ta’addanci da tunzura mutane.

Alƙalin kotun, Mai Shari’a James Omotosho ya ce laifukan Kanu sun cancanci hukuncin kisa ne, amma ya ce kasashena ƙasashen duniya suna nuna rashin jin daɗi kan hukuncin kisa, sai ya mayar da hukuncin na ɗaurin rai da rai.

Sai dai alƙalin ya ce a nema wa Kanu wani gidan yarin daban ba na Kuje da ke Abuja saboda a cewarsa yana da hatsari, sannan ya haramta masa amfani da waya da sauran na’urorin sadarwa, inda ya ce idan ma zama dole sai ya yi, “to ya kasance ana sa masa ido sosai,” in ji alƙalin.

Tuhume-tuhumen da ake yi wa Kanu sun haɗa da ta’addanci da tunzura jama’a su kashe ƴansanda da sojoji da kasancewa mamba a haramtacciyar ƙungiyar IPOB da gwamnatin Najeriya ta haramta da kuma yaɗa farfagandar ta’addanci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp