Home General Gwamnatin Neja ta ɗora alhakin sace ɗalibai kan makarantar

Gwamnatin Neja ta ɗora alhakin sace ɗalibai kan makarantar

Afghan military personnel walk near the airport during fighting between Taliban militants and Afghan security forces in Kunduz on October 1, 2015. Afghan forces pushed into the centre of Kunduz on October 1, triggering pitched gunfights as they sought to flush out Taliban insurgents who held the northern city for three days in a stinging blow to the country's NATO-trained military The stunning fall of the provincial capital, even temporarily, highlighted the stubborn insurgency's potential to expand beyond its rural strongholds in the south of the country Afghan forces, hindered by the slow arrival of reinforcements but backed by NATO special forces and US air support, struggled to regain control of the city after three days of heavy fighting. AFP PHOTO / Wakil Kohsar

Gwamnatin jihar Neja da ɗora wa makarantar St Mary alhakin sace ɗaliban makarantar da ƴan bindiga suka yi a tsakar daren jiya Alhamis.

Cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar, ta ce rashin bin shawarar da ta bayar ne ya haifar da matsalar.

‘Dama tuni mun samu bayanan sirri game da barazanar tsaro a yankin – da ke yankin arewacin jihar, lamarin da ya sa muka ɗauki matakin rufe duka makarantun kwanan da ke yankin tare da dakatar da ayyukan gine-gine”. in ji sanarwar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa amma abin kaico sai hukumomin makarantar St. Mary suka yi gaban kansu suka sake buɗe makarantar ba tare da sanar da gwamnati ko neman sahalewa ba, inda suka jefa rayukan ɗalibai da malaman makarantar cikin hatsari.

Gwamnatin ta ce tuni ta ƙaddamar da bincike da ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban tare da maido da su cikin kwanciyar hankali.

”Gwamnatin jihar Neja na tuntuɓar jami’an tsaro kan matakan da ake ɗauka na kuɓutar da ɗaliban”, in ji Sanarwar.

Harin na zuwa ne kwana biyar da sace ɗaliban makarantar sakandiren ƴanmata da ke garin Maga a jihar Kebbi tare da sace ɗalibai fiye da 20.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp