Home General Kotu ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin daurin rai da rai

Kotu ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin daurin rai da rai

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin daurin rai da rai bisa samunsa da dukkan laifukan da ake tuhumarsa da su.

Kotun ta yanke masa hukuncin ne bayan samunsa da laifuka bakwai, waɗanda suke da alaƙa da ta’addanci da tunzura mutane.

Alƙalin kotun, Mai Shari’a James Omotosho ya ce laifukan Kanu sun cancanci hukuncin kisa ne, amma ya ce kasashena ƙasashen duniya suna nuna rashin jin daɗi kan hukuncin kisa, sai ya mayar da hukuncin na ɗaurin rai da rai.

Sai dai alƙalin ya ce a nema wa Kanu wani gidan yarin daban ba na Kuje da ke Abuja saboda a cewarsa yana da hatsari, sannan ya haramta masa amfani da waya da sauran na’urorin sadarwa, inda ya ce idan ma zama dole sai ya yi, “to ya kasance ana sa masa ido sosai,” in ji alƙalin.

Tuhume-tuhumen da ake yi wa Kanu sun haɗa da ta’addanci da tunzura jama’a su kashe ƴansanda da sojoji da kasancewa mamba a haramtacciyar ƙungiyar IPOB da gwamnatin Najeriya ta haramta da kuma yaɗa farfagandar ta’addanci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp