Home Labarai Gwamnatin Nasarawa za ta kafa ƴan sandan Jiha

Gwamnatin Nasarawa za ta kafa ƴan sandan Jiha

Gwamnatin jihar Nasarawa ta bayyana shirinta na kafa rundunar ‘yan sandan jiha idan kundin tsarin mulkin ƙasar ya amince da hakan.

Kalaman sun fito ne daga kwamishinan tsaro da harkokin sauran al’amura, CP Usman Baba yayin wani taron manema labarai a Lafia, babban birnin jihar.

Kwamishinan ya ce tun daga zuwan gwamnatin jihar a 2019, an fifita harkar tsaro, tare da ba rundunonin tsaro tallafi na ababen hawa da kayan aiki da sauran kayan aikace-aikace.

Ya jaddada cewa gwamna Abdullahi Sule ya ƙuduri aniyar tabbatar da cewa jihar ta kasance amintacciya ga masu zuba jari da kuma wuri mai cike da zaman lafiya ga al’ummarta.

Haka kuma, ya bayyana cewa an tura jami’an tsaro zuwa makarantu a yankunan da ake ganin barazana ce, da manyan wuraren ibada a babban birnin jihar da kuma dukkan ƙananan hukumomi 13 na jihar.

Game da matsalar garkuwa da mutane, kwamishinan ya ce gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro, ‘yan sa kai da masu sa ido a unguwanni domin magance lamarin.

Ya gargadi masu aikata laifi cewa jihar za ta zama “wuri mai zafi” gare su, inda duk wanda aka kama zai fuskanci hukunci mai tsanani.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp