Home Labarai Wadanda aka sace a Cocin jihar Kwara sun shaki iskar ‘yanci

Wadanda aka sace a Cocin jihar Kwara sun shaki iskar ‘yanci

Rahotanni na bayyana cewa masu bauta 38 da aka sace a cocin Kwara da ke ƙaramar hukumar Eruku a ranar 18 ga Nuwamba, 2025, harin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum uku tare da jikkatar wani sun koma gida lafiya bayan an kubutar da su.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙaramar hukumar Ekiti, Dada Sunday ya fitar a daren Talata, ya tabbatar da cewa gwamnan jihar, AbdulRahman AbdulRazaq ne ya miƙa waɗanda aka ceto ga shugaban ƙaramar hukumar Ekiti, Honourable Awelewa Olawale Gabriel, a birnin Ilorin.

Da yake karɓar wadanda aka ceto, Awelewa ya bayyana godiyarsa ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da gwamna AbdulRazaq da duka hukumomin tsaro bisa gaggawa da ƙoƙari wajen ceton mutanen.

Ya ce aikin haɗin gwiwar jami’an tsaro da gwamnati ya taimaka wajen kammala ceto cikin lokaci, tare da ba wa wanɗanda aka kuutar cikakkiyar kulawa.

Sanarwar ta ce tawagar waɗanda aka ceto ta isa garin Eruku da misalin ƙarfe 6:30 na yammacin Talata, inda dangi da mazauna yankin suka tarbe su cikin murna da farin ciki.

Shugaban ƙaramar hukumar ya tabbatar wa mazauna yankin cewa gwamnati za ta ci gaba da bai wa tsaro mahimmanci, tare da ƙarfafa matakan kare rayuka da dukiyoyi a dukkan gundumomi 10 na yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp