Home Labarai Majalisa ta amince da naɗin Chris Musa ministan tsaron Najeriya

Majalisa ta amince da naɗin Chris Musa ministan tsaron Najeriya

Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da naɗin Janar Christopher Musa a matsayin sabon ministan tsaro.

Zaman majalisar ya cika da ruɗani a yau Laraba yayin da wasu ‘yanmajalisar ke cewa janar ɗin, wanda shi ne tsohon babban hafsan tsaron Najeriya, ya rusuna ya wuce ba tare da amsa tambayoyi masu yawa ba, da kuma waɗanda suka ce dole sai ya amsa.

Daga ƙarshe dai Shugaban Majalisa Godswill Akpabio ya shawo kan hayaniyar kuma ya amince cewa akwai buƙatar Janar Musa mai ritaya ya amsa tambayoyin da suka dace.

Da yake jawabi, janar ɗin ya bayyana shirinsa na shawo kan matsalar tsaro, da kuma dawo da martabar rundunar sojin ƙasar a idon ‘yan Najeriya.

“Wannan ba lokaci ne na yin siyasar “rusuna ka wuce ba”. Hatta Donald Trump yana matsa mana. Ba game-garin mutum ba ne, tsohon babban hafsan tsaro ne,” kamar yadda Akpabio ya bayyana lokacin da ya miƙe daga kujerarsa lokacin da ake hayaniyar.

Ana sa ran Janar Musa zai fara aiki nan take bayan Mohammed Badaru ya sauka daga muƙamin a ranar Litinin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp