Home Labarai Amnesty ba bukaci a gaggauta sakin Muhuyi Magaji

Amnesty ba bukaci a gaggauta sakin Muhuyi Magaji

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty international tayi Allah wadai da abin da ta kira tauye hakkin dan adam da rundunar ‘yan sanda Nijeriya ke ci gaba da yiwa tsohon shugaban hukumar yaki da cin hanci da karbar korafe korafe ta jihar Kano Muhuyi magaji Rimin Gado.

Ta cikin wani sautin murya da shugaban hukumar gudanarwa ta kungiyar ya aikewa PRNigeria Hausa, ya bayyana cewa kungiyar ta yi tofin alatsine kan yadda ake ci gaba da musgunawa gami da tauyi hakkin Muhuyi duk dace doka bata bawa ‘yan sandan damar kama shi ba, haka kuma babu wata kotu da ta bada umarnin yin kamun.

Kungiyar ta bukaci rundunar ‘yan sandan Nijeriya da ta gaggauata sakin Muhuyi tare kuma da daina cin zarafinsa da sauran Al’ummar Nijeriya.

Ba dai wannan ne karon barko da dakarun ‘yan sandan ke yiwa Muhuyi wannan kamu ba, duk da cewa ana kallon hakan na da nasaba da takun saka da yake fuskanta da wasu ‘yan siyasa a jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp