Home General Kwankwaso ya ce matsalar tsaro na neman fin karfin Gwamnatin Nijeriya

Kwankwaso ya ce matsalar tsaro na neman fin karfin Gwamnatin Nijeriya

Jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya nuna matuƙar damuwa kan yadda matsalar tsaro ke ta ’kara munana a Najeriya, yana mai gargaɗin cewa matsalolin tsaro da ke faruwa yanzu na neman ya fi ƙarfin gwamnati.

Ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.

Kwankwaso, wanda ya taɓa zama gwamnan Kano, ya ce alamu na nuna cewa matsalolin tsaro da ke faruwa yanzu ka iya zama babbar barazana ga haɗin kai da kwanciyar hankalin ƙasa.

A cikin saƙonsa, ya ce: “Dukkan alamu na nuna cewa rashin tsaro na neman ya fi ƙarfin gwamnatin. Wannan na bayyana a yadda take barin jihohi su kafa ƙungiyoyin tsaro na ƴan sa kai ba tare da horo na musamman ba.”

“Wannan mataki, ko da an yi shi da kyakkyawar niyya, ya haddasa yaɗuwar ƙananan makamai da manyan makamai a faɗin ƙasa.” in ji shi.

Kwankwaso ya kuma nuna damuwa kan yadda ake samun ƙaruwa a tsangwama da azabtar da ’yan Najeriya musamman daga wasu yankuna.

Ya ce “wasu ’yan siyasa ma sun fara amfani inda ya ƙara da cewa kalaman ƙiyayya a kafofin sada zumunta na ƙara rura wutar rikici da raba kan al’umma.

Kwankwaso ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta hanzarta ɗaukar mataki kafin lamura su lalace gaba ɗaya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp