Home Labarai Za mu ci gaba da kamen masu bakin gilashin mota – Yan...

Za mu ci gaba da kamen masu bakin gilashin mota – Yan sanda

Ƴansandan Najeriya sun sanar da cewa za su ci gaba da tilasta bin dokar mallakar lasisin amfani da gilashin mota mai duhu ko kuma su ci gaba da kame daga 2 ga Janairu 2026, abin da ya janyo suka daga ƙungiyar lauyoyin Najeriya (NBA), wadda ta bayyana matakin a matsayin saɓa wa hukuncin kotu da kuma tauye doka.

Wannan sanarwa ta fito ne daga CSP Benjamin Hundeyin, jami’in hulɗa da jama’a na hukumar ƴan Sanda, a ranar 15 ga Disamba 2025.

NBA ta bayyana cewa matakin ƴansandan ya saɓawa hukuncin da kotu ta yanke inda ta dakatar da aiwatar da dokar har sai an gama shari’ar ƙarar ƴansandanda aka shigar a gabanta na ƙalubalantar halaccin dokar.

Lauyoyi sun yi gargadi cewa wannan mataki zai ƙara nauyi ne ga talakawa, kuma zai iya jawo cin hanci da rashawa.

Wannan lamarin ya fara ne a watan Afrilu 2025 lokacin da rundunar ƴansandan Najeriya ta shigo da dokar mallakar lasisin gilashin mota mai duhu, wacce ta bukaci ‘yan Najeriya su yi rijista ta intanet domin samun lasisi inda aka tsara fara aiwatar da dokar a ranar 1 ga Yuni 2025, daga baya aka ɗage zuwa 2 ga Oktoba saboda korafe-korafe da dama daga jama’a.

NBA ta buƙaci ƴansandan da su dakatar da duk wani mataki na ci gaba da aiwatar da dokar har sai kotu ta yanke hukunci na ƙarshe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp