Home Labarai Sojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a Borno

Sojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a Borno

Nigerian Army

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na Operation Haɗin Kai daƙile yaƙunrin hain ƴanbindiga ina sun kashe su daga tsaunukan Mandara a lokacin da suka yunƙurin kai hari a cikin al’ummar Bitta da ke Borno.

Rundunar ce ta sanar da hakan a shafinta na X inda ta ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12:30 na tsakar daren ranar 18 ga Disamba, 2025 lokacin da sojojin suka gano wannan yunƙuri na ‘yanbindig da ke tafiya zuwa yankin.

A cewar rundunar, sai da sojojin suka bari ƴanbindigar suka shiga wani yanki da aka musu tarko kafin buɗe musu wuta, inda suka kashe wasu daga cikin maharan, ciki har da wani kwamandansu da mai ɗaukar musu hoto.

Rundunar ta ƙara da cewa, daga baya rundunar sojojin sama ta Operation Haɗin Kai ta kai farmaki kan waɗanda suka tsere lamarin da ya ƙara hallaka wasu tare da tarwatsa hanyoyin gudunsu.

A lokacin da ake fafatawa a yankin, an ruwaito cewa sojoji sun bi diddigin hanyoyi da dama, kuma sun gano kaburbura marasa zurfi, wanda ke nuna ƙarin asarar rayuka da aka yi wa ‘yan ta’addan a lokacin fafatawar.

Bayan fafatawar, sojoji sun gudanar da bincike a yankin inda suka ƙwato kayayyaki da makamai da dama.

Rundunar ta ce sojoji na ci gaba da ayyukansu domin hana masu ta da ƙayar baya samun damar kai hari, tare da tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp