Home Labarai An samu gagarumar raguwar matsalar tsaro a Zamfara – Sojoji

An samu gagarumar raguwar matsalar tsaro a Zamfara – Sojoji

Babban kwamandan runduna da ɗaya ta sojin Najeriya da ke Gusau, Birgediya Janar Mustapha Jimoh, ya ce ayyukan ƴanbindiga da ƴanta’adda a jihar Zamfara sun yi matuƙar raguwa.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai a wani taro na musamman da rundunar ta shirya a birnin Gusau, Janar Jimoh ya ce hare-haren soji a jihar ƙarƙashin rundunar Fansan Yamma sun yi matuƙar inganta tsaro da zaman lafiya a jihar, kamar yadda gidan talbijin na Channels ya ruwaito.

Janar Jimo ya ƙara da cewa matakin ya sa a yanzu mazauna jihar da matafiya za su yi tafiye-tafiyensu cikin kwanciyar hankali ba tare da fargabar hare-haren ƴanbindiga ba.

“Za ku iya zama shaida a yanzu za ku iya yin tafiya daga Funtua zuwa Gusau, ko Gusau zuwa Sokoto ba tare da wata fargaba ba, don haka za mu iya cewa an samu gagarumar raguwar matsalar tsaro a jihar Zamfara”, in ji shi.

Kwamandan rundunar sojin ya ce rundunarsa za ta ci gaba da ƙoƙari wajen kakkaɓe ragowar ayyukan ƴanbindigar ba a Zamfara kawai ba, har ma da sauran jihohin arewa maso yammacin Najeriya da ma ƙasar baki ɗaya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp