Home Labarai Likitoci sun manta almakashi a cikin wata mata a Kano

Likitoci sun manta almakashi a cikin wata mata a Kano

‘Yan uwan wata mata Aishatu Umar, sun koka kan yadda suke zargin likitoci a asibitin Abubakar Imam sun manta Almakashi a Cikin ‘yar’uwarsu, abin da yayi sanadiyyar mutuwarta.

Ta cikin wani rubutu a shafin facebook da Abubakar Muhammad, ɗan’uwa ga marigayiyar ya wallafa, ya zargi sakacin likitocin matsayin abin da yayi sanadiyyar mutuwarta.

Yace a watan Satumbar daya gabata ne, aka yiwa Aisha aikin tiyata a Asibitin ƙwararun na Abubakar Imam dake Kano, al’amarin da daga baya ha dinga haifar mata da matsanancin ciwon mara.

Bayan ƙorafe-ƙorafe da yace mariganyar ta yi ga likitocin asibitin lokuta da dama amman suna nuna ba wata matsala, sai daga baya suka yanke shawarar zuwa a ɗau gwajin hoton cikin, inda anan ne aka gane almakashin fiɗa aka bari a cikinta bayan tiyatar. Gano hakan ya faru ne kwanaki biyu kafin rasuwarta.

Sai dai bayan fitar labarin, hukumar dake lura da asibitocin jihar Kano ta bayar da umarnin gudanar da bincike akan lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp