Home Labarai Sojojin sun gano makeken kabarin ƴan Boko Haram a yankin Timbuktu

Sojojin sun gano makeken kabarin ƴan Boko Haram a yankin Timbuktu

Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa sojojin haɗin gwiwarta na Operation Haɗin kai da JTF sun gano wani makeken kabarin wasu mayaƙan Boko Haram a yankin Timbuktu, wanda aka ƙiyasta yana ɗauke da gawarwaki guda 20 da aka kashe.

Sanarwar rundunar ta ce wannan kabarin an gano shi ne yayin da sojoji ke ci gaba da ayyukan samame da ragargazar ‘yanbindiga a yankin, musamman a wani tashar jiragen ruwa da ke kilomita 6 arewa da Chilaria.

A yayin samamen, sojojin sun gamu da motoci biyu masu ɗauke da abubuwan fashewa.

Duk da cewa sun samu nasarar kawar da ɗaya daga cikin motocin, ɗayan motar ta fashe, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar wasu daga cikin sojojin da kuma raunata wasu.

An gaggauta ɗaukar waɗanda suka ji rauni zuwa asibiti domin samun kulawa, yayin da rundunar ke ci gaba da ayyukanta na tabbatar da tsaro a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp