Home Labarai Abba da Tinubu sun tattauna kan tsaro da ci gaban Kano –...

Abba da Tinubu sun tattauna kan tsaro da ci gaban Kano – Dawakin Tofa

Gwamnatin jihar Kano ta fitar da wata sanarwa domin yin ƙarin haske kan ganawar da gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ya yi da shugaban Najeriya Bola Tinubu.

A yammacin Litinin ne gwamnan, wanda aka daɗe ana raɗe-raɗin komawarsa jam’iyyar APC mai mulki daga jam’iyyar NNPP ya gana da Bola Tinubu, inda ake sa ran cewa tattaunawar ta ƙunshi batun cimma yarjejeniya kan sauya sheƙar gwamnan.

Sai dai a sanarwar da gwamnatin ta fitar ta hannun mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature, ta ce gwamnan da shugaban ƙasa sun tattauna ne kan muhimman abubuwa da suka shafi tsaro da samar da ayyukan more rayuwa.

Sanarwar ta ce ganawar, wadda aka yi a asirce, “ta bai wa gwamnan damar yi wa shugaban ƙasa bayani kan manyan ƙalubale da jihar Kano ke fuskanta musamman taɓarɓarewar tsaro a wasu ƙananan hukumomi.

“Gwamna Yusuf ya kuma yi wa shugaban ƙarin bayani kan matar da aka kashe da ’ya’yanta shida kwanan nan, yana mai jaddada buƙatar gaggawar tallafin gwamnatin tarayya domin ƙarfafa ayyukan tsaro da kare rayukan fararen hula.

“Ya kuma bayyana rawar da Rundunar Tsaro ta Jihar Kano ke takawa wajen taimaka wa hukumomin tsaro, tare da neman ƙarin haɗin gwiwa da hukumomin tsaron tarayya.

“A ɓangaren raya ƙasa, gwamnan ya tattauna manufar ci gaban Kano, inda ya mayar da hankali kan manyan ayyukan gine-gine.

“A nasa ɓangaren, Shugaba Tinubu ya tabbatar wa gwamnan cewa “gwamnatin tarayya a shirye take ta yi aiki kafaɗa da kafaɗa da Kano domin shawo kan matsalolin tsaro da kuma tabbatar da ci gaba mai ɗorewa,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp