Home Labarai Sojojin sun gano makeken kabarin ƴan Boko Haram a yankin Timbuktu

Sojojin sun gano makeken kabarin ƴan Boko Haram a yankin Timbuktu

Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa sojojin haɗin gwiwarta na Operation Haɗin kai da JTF sun gano wani makeken kabarin wasu mayaƙan Boko Haram a yankin Timbuktu, wanda aka ƙiyasta yana ɗauke da gawarwaki guda 20 da aka kashe.

Sanarwar rundunar ta ce wannan kabarin an gano shi ne yayin da sojoji ke ci gaba da ayyukan samame da ragargazar ‘yanbindiga a yankin, musamman a wani tashar jiragen ruwa da ke kilomita 6 arewa da Chilaria.

A yayin samamen, sojojin sun gamu da motoci biyu masu ɗauke da abubuwan fashewa.

Duk da cewa sun samu nasarar kawar da ɗaya daga cikin motocin, ɗayan motar ta fashe, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar wasu daga cikin sojojin da kuma raunata wasu.

An gaggauta ɗaukar waɗanda suka ji rauni zuwa asibiti domin samun kulawa, yayin da rundunar ke ci gaba da ayyukanta na tabbatar da tsaro a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp