Home Labarai Gwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan Siyasa

Gwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan Siyasa

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya cire Sunusi Surajo Kwankwaso daga mukamin mai ba shi shawara kan harkokin siyasa tare da maye gurbinsa da Mustapha Buhari Bakwana.

Hakan na cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran Gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Idan za’a iya tunawa Sunusi Surajo Kwankwaso ya bayyana cewa ya kai takardarsa ta ajiye aiki amma anki karbar, wanda ya ce hakan ce tasa a fito fili ya fadawa Duniya cewa ya ajiye mukamin nasa.

Sunusi Surajo Kwankwaso dai na daga cikin wadanda tun a tashin fari suka nuna cewa za su kasance tare da madugun Kwankwasiyya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Wannan dambarwar dai ta Sami asali ne tun lokacin da aka fara jita-jitar gwamnan Kano zai raba gari da ubangisansa na Siyasa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Bakwana dai ya taba rike wannan mukamin lokacin mulkin Dr. Abdullahi Umar Ganduje yana gwamnan Kano.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp