Home Labarai NNPCL zai dauko ƙwararru daga chaina domin inganta Matatun kasar

NNPCL zai dauko ƙwararru daga chaina domin inganta Matatun kasar

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ce yana tattaunawa da wata matatar man fetur a ƙasar China domin inganta matatun man fetur na Najeriya.

Babban jami’in gudanarwa na kamfanin, Bayo Ojulari ne ya bayyana haka a ranar Laraba, inda ya ce suna buƙatar ƙwararru ne domin mayar da matatun gwamnatin ƙasar su koma aiki da kyau bayan shekarun da suka ɗauka ba sa aiki yadda ya kamata.

Ojulari ya ce nazarin da suka gudanar bayan ya fara aiki ne suka gano cewa ana asarar kuɗi ne maimakon cin riba wajen gudanar da matatun.

Ya ce sun amince da ɗauko ƙwararru waɗanda suka san aikin ɓangaren, maimakon ɗauko ƴan kwangila.

“Shirye-shirye sun yi nisa. Muna ci gaba da tattaunawa da wasu ƙwararru da muke so su inganta mana ayyukan matatun. Kuma gobe wasu daga ciki za su fara zuwa matatun.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp