Hukumar Hisbah a jihar Kano ta ce jami’anta sun kama wasu mutum tara Musulmai a jiya Laraba a take ranar farko ta azumin watan Ramadan saboda an gan su suna cin abinci da tsakar rana.
Jihar Kano na da yawan Musulmai, inda tsarin shari’ar Musulunci ke aiki tare da dokokin ƙasa na yau da kullum.
A kowane Ramadan, Hisbah na bincika wuraren sayar da abinci da kasuwanni domin tabbatar da cewa Musulmai na bin dokokin azumi.
A wasu wurare, wurarern cin abinci na ci gaba da aiki musamman a yankunan da Kiristoci da dama ke zaune.
Ga Musulmai masu azumi, cin abinci daga fitowar rana zuwa faduwar rana haramun ne.
Yin azumi na daga cikin ginshikan Musulunci guda biyar da ke kafa yadda Musulmai ke gudanar da rayuwarsu.
Mujahid Aminudeen, mataimakin kwamandan Hisbah, ya shaida wa BBC cewa daga cikin wadanda aka kama akwai mata biyu da maza bakwai.
Ya ce: “Mun kama su kuma suna tare da mu inda za mu koya musu muhimmancin azumi, yadda za su yi salla da karanta Al-Qur’ani, kuma su zama Musulmai nagari.”
Ba a bayyana lokacin da Hisbah za ta saki wadanda aka kama ba.











