Home Labarai Masu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a Filato

Masu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a Filato

Aƙalla masu haƙar ma’adinai 33 ne suka mutu sakamakon shakar iskar gas ta sinadarin carbon wace take guba mai ƙarfi yayin da suke hakar ma’adinai a Jihar Plateau, kamar yadda bbc ta rawaito.

Ana hasashen wannan mummunan lamari ya faru ne kafin fitowar rana a wani wuri a wajen garin Wase, wanda kamfanin ma’adinai na Solid Unity Nigeria Ltd, ke gudanarwa.

Ana ganin cewa guba mai ƙarfi ta sinadarin ta taru a cikin ramin ƙasa da iska ba ta samun shiga sosai, wanda ya sa ma’aikatan suka fadi a kasa kafin su kammala aikin dare.

Wadanda suka je aiki da safe ne suka tarar da gawawwakin.

Jami’an tsaro sun rufe wurin hakar ma’adinan, wanda ke kimanin kilomita 200 daga gabas zuwa kudu maso gabas na Jos, babban birnin Jihar Plateau, yayin da ake gudanar da bincike domin gano musabbabin zubar sinadarin.

Hukumomin jihar har yanzu ba su kai ziyara wurin ba, kuma rahotanni sun nuna cewa an samu cikkas wajen kai taimakon gaggawa saboda rashin tsaro a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp