Dakarun sojojin Najeriya karkashin Operation HADIN KAI sun sami wannan nasara ne sakamakon wani sumame da suka kai domin dakile ayyukan mayaƙan Boko Haram a yankin Arewa maso gabashin Ƙasar.
A sumamen sun sami nasarar hallaka mayakan ƙungiyar Boko Haram biyu ciki harda kwamandanta Abdullahi Mafa, wanda ya jima yana jagorantar hare- hare a yankin Madagali
Read Also:
Wata majiyar tsaro ta shaida cewa da misalin karfe 5:30am ranar Alhamis sojojin haɗin gwiwa da Jami’an bijilanti da mafarauta suka aikawa mabiyan ƴan ta’addan kusa da kogin Visil a karamar hukumar Mafarki dake jihar.
Haka kuma dakarun sun tasamma tashar mota ta Madagali da misalin karfe 6:30 inda suka kama wani mutum mai kimanin shekaru 64 mai suna Dauda Usman wanda ke matsayin mai sayarwa da ƴan Boko Haram jirgi maras matuka wai Done da wasu kayayyakin amfanin yau da kullum.











