Home Labarai Sojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da...

Sojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a Adamawa

Dakarun sojojin Najeriya karkashin Operation HADIN KAI sun sami wannan nasara ne sakamakon wani sumame da suka kai domin dakile ayyukan mayaƙan Boko Haram a yankin Arewa maso gabashin Ƙasar.

A sumamen sun sami nasarar hallaka mayakan ƙungiyar Boko Haram biyu ciki harda kwamandanta Abdullahi Mafa, wanda ya jima yana jagorantar hare- hare a yankin Madagali

Wata majiyar tsaro ta shaida cewa da misalin karfe 5:30am ranar Alhamis sojojin haɗin gwiwa da Jami’an bijilanti da mafarauta suka aikawa mabiyan ƴan ta’addan kusa da kogin Visil a karamar hukumar Mafarki dake jihar.

Haka kuma dakarun sun tasamma tashar mota ta Madagali da misalin karfe 6:30 inda suka kama wani mutum mai kimanin shekaru 64 mai suna Dauda Usman wanda ke matsayin mai sayarwa da ƴan Boko Haram jirgi maras matuka wai Done da wasu kayayyakin amfanin yau da kullum.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp