Home Labarai Gwamnatin Nijeriya Na Shirin Yiwa ASUU Kishiya

Gwamnatin Nijeriya Na Shirin Yiwa ASUU Kishiya

Ministan kwadago da samar da aikin yi na Najeriya, Chris Ngige ya damka takardar shaida ga kungiyar ma’aikatan koyarwa a jami’o’in Najeriya, wadda kungiya ce ta malaman jami’o’in tarayya da na jihohi.

Kungiyar mai suna CONUA a takaice ana ganin kai tsaye za ta kasance kishiya ga babbar kungiyar malaman jami’o’in Najeriya wato ASUU.

Wani jami’in gwamnatin Najeriya ya wallafa cewa an kafa kungiyar CONUA ne a shekara ta 2018 a jami’ar jihar Osun.

Kungiyar ASUU da gwamnatin Najeriya na kai ruwa rana saboda yajin aikin sai-baba-ta-gani da malaman jami’o’in suka shiga tsawon wata takwas ke nan yanzu, suna neman sai lallai gwamnati ta biya musu bukatunsu.

Duk da wani kokari da ban-baki da tattaunawa daga gwamnati sun kasa shawo kan kungiyar malaman kungiyar ASUU dakatar da yajin aiki.

Baya ga kungiyar CONUA, ministan kwadagon ya kuma amince da kungiyar likitoci masu koyarwa ta kasa (NAMDA)

an dai sami tirka-tirka tsakanin kungiyar malaman jami’ar ta ASUU da Gwamnatin tarayya Nijeriya, duk da cewa sun zauna zaman sulhu a tsakani amma ana kallon hakan yaci tura, ko da yake ana kallon samar da wannan kungiyar matsayin wani matashi na rage karfin kungiyar malaman ta ASUU.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp