Home Labarai Gwamnatin Jihar Zamfara ta Amince da Biyan Naira Dubu 30 Matsayin Mafi...

Gwamnatin Jihar Zamfara ta Amince da Biyan Naira Dubu 30 Matsayin Mafi Karancin Albashi

Gwamnatin jihar Zamfara ta amince ta aiwatar da mafi karancin albashin naira dubu 30 ga ma’aikatan jihar.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwar da babban daraktan yada labarai na ofishin mataimakin gwamna, Babangida Umar, ya fitar ranar Laraba a Gusau, babban birnin jihar, sanarwar tace mataimakin gwamna, Sanata Hassan Nasiha, ya sanar da hakan ne yayin karbar takardar yarjejeniyar da gwamnati ta kulla da ma’aikatan.

Mataimakin gwamnan ya nuna jin dadinsa game da yadda kungiyar kwadago ta nuna girma da fahimta yayin yarjejeniya da ma’aikatan gwamnati.

Fahimtarsu ta sa aka yanke shawarar aiwatar da mafi karancin albashi na N30,000 a watan Nuwamba.

“Halin da ake ciki na tabarbarewar tattalin arziki da kalubalen tsaro na cikin abubuwan da gwamnati ta yi la’akari da su kafin ta amince da aiwatar da sabon albashin,” in ji shi.

Ya kuma yaba wa kwamitin da Ambasada Bashir Yuguda ya jagoranta da ya wakilci gwamnati wajen cimma matsaya da kungiyoyin kwadago cikin lumana.

(NAN)

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp