Gwamnatin Jihar Zamfara ta Amince da Biyan Naira Dubu 30 Matsayin Mafi Karancin Albashi

Gwamnatin jihar Zamfara ta amince ta aiwatar da mafi karancin albashin naira dubu 30 ga ma’aikatan jihar.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwar da babban daraktan yada labarai na ofishin mataimakin gwamna, Babangida Umar, ya fitar ranar Laraba a Gusau, babban birnin jihar, sanarwar tace mataimakin gwamna, Sanata Hassan Nasiha, ya sanar da hakan ne yayin karbar takardar yarjejeniyar da gwamnati ta kulla da ma’aikatan.

Mataimakin gwamnan ya nuna jin dadinsa game da yadda kungiyar kwadago ta nuna girma da fahimta yayin yarjejeniya da ma’aikatan gwamnati.

Fahimtarsu ta sa aka yanke shawarar aiwatar da mafi karancin albashi na N30,000 a watan Nuwamba.

“Halin da ake ciki na tabarbarewar tattalin arziki da kalubalen tsaro na cikin abubuwan da gwamnati ta yi la’akari da su kafin ta amince da aiwatar da sabon albashin,” in ji shi.

Ya kuma yaba wa kwamitin da Ambasada Bashir Yuguda ya jagoranta da ya wakilci gwamnati wajen cimma matsaya da kungiyoyin kwadago cikin lumana.

(NAN)

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 29 minutes 39 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 11 minutes 4 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com