Home Labarai Zaɓen gwamnan Kebbi bai Kammala ba – INEC

Zaɓen gwamnan Kebbi bai Kammala ba – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya ta bayyana sakamakon zaɓen gwamnan jihar Kebbi a matsayin wanda bai kammala ba.

Babban jami’in tattara sakamakon zaɓen jihar Farfesa Yusuf Sa’idu na jami’ar Usman Danfodio da ke Sokoto ne ya bayyana haka a cibiyar karɓar sakamakon zaɓen da ke Birnin Kebbi.

Ya ce an samu yawan ƙuri’u da aka soke a rumfunan zaɓe da dama a faɗin ƙananan hukumomi 20, daga cikin 21 na jihar.

Fafatawar dai ta fi zafi ne tsakanin manyan jam’iyyun APC mai mulkin jihar da kuma jam’iyyar PDP mai hamayya.

Farfesa Sa’idu ya ce adadin katin zaɓen da aka karɓa a wuraren da aka soke zaɓen ya kai 91,829.

“Sakamakon da muka tattara yanzu ya nuna cewa jam’iyyar APC na da yawan ƙuri’u 388,258, yayin da PDP ke da ƙuri’a 342,980. Dan haka idan muka duba bambancin da ke tsakaninsu shi ne ƙuri’a 45,278,” in ji Farfesa Sa’idu.

Dan haka a cewarsa ba abin da ya kamata a yi sai komawa sashe 51 ƙaramin sashen biyu da na uku, na dokar zaɓe ta 2022.

Wanda ya tanadi cewa idan adadin ƙuri’un da aka soke ya zarta adadin tazarar ƙuri’un da ke tsakanin ‘yan takara to dole sai an sake zaɓe a wuraren da aka soke zaɓukan.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp