Home Labarai Dan takarar Jam’iyyar LP a zauren majalisar Jihar legas bai ji rauni...

Dan takarar Jam’iyyar LP a zauren majalisar Jihar legas bai ji rauni ba, Bincike PRNigeria

Wani bincike da jaridar PRNigeria ta gudanar ya tabbatar da cewa Dan takarar jam’iyyar Labour Party na mazabar Surulere a zauren majalisar jihar Legas, Olumide Oworu, bai ji ciwo ba a zaben daya gabata ranar asabar.

Idan za’a iya tunawa an ta yada wani hoto a shafin Facebook na Oworu da yake nuna yadda yake zubar da jini a yanar gizo yana mai bayyana cewa an kai masa hari shi da tawagar sa abinda ya haddasa masa jikka a yayin zaben.

Haka kuma an ta yada hotunan a kafafen sada zumunta na zamani ciki har da shafin WhatsApp

amma PRNigeria tayi amfani da manhajar binciken hoto ta “reverse image search” kan hoton na Oworu.

Sakamakon ya nuna cewa Oworu da kan ne y afara wallafa hoton da jini a jikin sa a shafukan sada zumunta tun a watan Oktoban shekarar 2022, mai taken “Alagbado John Wick #OntheEdge,”

Haka kuma wani sakamako ya nuna makamancin hoton na dankarar majalisar jihar karkashin inuwar jam’iyyar LP a shafin Instagram na fitacciyar mai yin kwalliya, Carina Ojoko.

PRNigeria ta gano cewa wannan hoton an samo shi ne a cikin wani Shirin wasan kwakwayo mai suna “ On the Edge” bashi da hadi da harin kwanannan da aka ce an kaiwai dan takarar.

Dan haka dangane da binciken da PRNigeria ta gunadar, wannan hoton Olumide Oworu ya fito ne daga wani shiri na “On the Edge,” ba a lokacin harin aka samo shi ba.

Wannan ya sanya PRNigeria ta bayyana labarin matsayin na karlya da kanzon kurege.

PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp