Home Labarai Dan takarar Jam’iyyar LP a zauren majalisar Jihar legas bai ji rauni...

Dan takarar Jam’iyyar LP a zauren majalisar Jihar legas bai ji rauni ba, Bincike PRNigeria

Wani bincike da jaridar PRNigeria ta gudanar ya tabbatar da cewa Dan takarar jam’iyyar Labour Party na mazabar Surulere a zauren majalisar jihar Legas, Olumide Oworu, bai ji ciwo ba a zaben daya gabata ranar asabar.

Idan za’a iya tunawa an ta yada wani hoto a shafin Facebook na Oworu da yake nuna yadda yake zubar da jini a yanar gizo yana mai bayyana cewa an kai masa hari shi da tawagar sa abinda ya haddasa masa jikka a yayin zaben.

Haka kuma an ta yada hotunan a kafafen sada zumunta na zamani ciki har da shafin WhatsApp

amma PRNigeria tayi amfani da manhajar binciken hoto ta “reverse image search” kan hoton na Oworu.

Sakamakon ya nuna cewa Oworu da kan ne y afara wallafa hoton da jini a jikin sa a shafukan sada zumunta tun a watan Oktoban shekarar 2022, mai taken “Alagbado John Wick #OntheEdge,”

Haka kuma wani sakamako ya nuna makamancin hoton na dankarar majalisar jihar karkashin inuwar jam’iyyar LP a shafin Instagram na fitacciyar mai yin kwalliya, Carina Ojoko.

PRNigeria ta gano cewa wannan hoton an samo shi ne a cikin wani Shirin wasan kwakwayo mai suna “ On the Edge” bashi da hadi da harin kwanannan da aka ce an kaiwai dan takarar.

Dan haka dangane da binciken da PRNigeria ta gunadar, wannan hoton Olumide Oworu ya fito ne daga wani shiri na “On the Edge,” ba a lokacin harin aka samo shi ba.

Wannan ya sanya PRNigeria ta bayyana labarin matsayin na karlya da kanzon kurege.

PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp