Home Labarai Gawuna zai je Kotu domin kalubalantar nasarar Abba gida-gida

Gawuna zai je Kotu domin kalubalantar nasarar Abba gida-gida

Mataimakin gwamnan jihar Kano kuma ‘dan takarar Jam’iyyar APC a zaben da aka yi ranar Asabar, Dakta Nasir Yusuf Gawuna ya ce, hukumar zabe ta yi kuskure wajen bayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar sakamakon soke zaben wasu mazabun da aka yi.

ya bayyana hakan ne Yayin da yake ganawa da manema labarai, inda ya ce yawan akwatunan da aka soke ya kai ace hukumar zabe ta sake gudanar da zabuka a wuraren kafin gabatar da kammalallen sakamako da kuma sanar da wanda ya ci.

Mataimakin gwamnan ya ce lura da yadda hukumar zaben ta bayyana zaben ‘yan majalisun jihar Kano 16 a matsayin wadanda ba su kammala ba, wato ‘inconclusive’ ya dace ace ta dauki wannan mataki a zaben kujerar gwamnan.

Gawuna ya ce suna da yakinin cewar Allah ke bada mulki ga wanda ya so a lokacin da yake so, saboda haka za su bi matakan da suka dace ta fannin shari’a domin neman hakkinsu.

Mataimakin gwamnan ya jinjina wa mutanen Kano akan irin goyan bayan da suka ba shi, yayin da ya bukaci kwantar da hankali da kuma kauce wa daukar doka a hannu.

Shi ma a nasa jawabi, shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai ta kasa Hon. Alhassan Ado Doguwa ya ce dokar zabe ta yi tanadin cewar, idan an soke zabe a wasu mazabun da kan iya shafar kammalalen sakamakon baki daya, ya zama wajibi a koma domin sake gudanar da zabe a wadannan wurare kafin gabatar da kammalallen sakamako.

Ita dai hukumar zabe ta bayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan da kuri’u sama da miliyan guda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp