Home Labarai Gawuna zai je Kotu domin kalubalantar nasarar Abba gida-gida

Gawuna zai je Kotu domin kalubalantar nasarar Abba gida-gida

Mataimakin gwamnan jihar Kano kuma ‘dan takarar Jam’iyyar APC a zaben da aka yi ranar Asabar, Dakta Nasir Yusuf Gawuna ya ce, hukumar zabe ta yi kuskure wajen bayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar sakamakon soke zaben wasu mazabun da aka yi.

ya bayyana hakan ne Yayin da yake ganawa da manema labarai, inda ya ce yawan akwatunan da aka soke ya kai ace hukumar zabe ta sake gudanar da zabuka a wuraren kafin gabatar da kammalallen sakamako da kuma sanar da wanda ya ci.

Mataimakin gwamnan ya ce lura da yadda hukumar zaben ta bayyana zaben ‘yan majalisun jihar Kano 16 a matsayin wadanda ba su kammala ba, wato ‘inconclusive’ ya dace ace ta dauki wannan mataki a zaben kujerar gwamnan.

Gawuna ya ce suna da yakinin cewar Allah ke bada mulki ga wanda ya so a lokacin da yake so, saboda haka za su bi matakan da suka dace ta fannin shari’a domin neman hakkinsu.

Mataimakin gwamnan ya jinjina wa mutanen Kano akan irin goyan bayan da suka ba shi, yayin da ya bukaci kwantar da hankali da kuma kauce wa daukar doka a hannu.

Shi ma a nasa jawabi, shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai ta kasa Hon. Alhassan Ado Doguwa ya ce dokar zabe ta yi tanadin cewar, idan an soke zabe a wasu mazabun da kan iya shafar kammalalen sakamakon baki daya, ya zama wajibi a koma domin sake gudanar da zabe a wadannan wurare kafin gabatar da kammalallen sakamako.

Ita dai hukumar zabe ta bayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan da kuri’u sama da miliyan guda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp