Home Labarai Dan takarar Jam’iyyar LP a zauren majalisar Jihar legas bai ji rauni...

Dan takarar Jam’iyyar LP a zauren majalisar Jihar legas bai ji rauni ba, Bincike PRNigeria

Wani bincike da jaridar PRNigeria ta gudanar ya tabbatar da cewa Dan takarar jam’iyyar Labour Party na mazabar Surulere a zauren majalisar jihar Legas, Olumide Oworu, bai ji ciwo ba a zaben daya gabata ranar asabar.

Idan za’a iya tunawa an ta yada wani hoto a shafin Facebook na Oworu da yake nuna yadda yake zubar da jini a yanar gizo yana mai bayyana cewa an kai masa hari shi da tawagar sa abinda ya haddasa masa jikka a yayin zaben.

Haka kuma an ta yada hotunan a kafafen sada zumunta na zamani ciki har da shafin WhatsApp

amma PRNigeria tayi amfani da manhajar binciken hoto ta “reverse image search” kan hoton na Oworu.

Sakamakon ya nuna cewa Oworu da kan ne y afara wallafa hoton da jini a jikin sa a shafukan sada zumunta tun a watan Oktoban shekarar 2022, mai taken “Alagbado John Wick #OntheEdge,”

Haka kuma wani sakamako ya nuna makamancin hoton na dankarar majalisar jihar karkashin inuwar jam’iyyar LP a shafin Instagram na fitacciyar mai yin kwalliya, Carina Ojoko.

PRNigeria ta gano cewa wannan hoton an samo shi ne a cikin wani Shirin wasan kwakwayo mai suna “ On the Edge” bashi da hadi da harin kwanannan da aka ce an kaiwai dan takarar.

Dan haka dangane da binciken da PRNigeria ta gunadar, wannan hoton Olumide Oworu ya fito ne daga wani shiri na “On the Edge,” ba a lokacin harin aka samo shi ba.

Wannan ya sanya PRNigeria ta bayyana labarin matsayin na karlya da kanzon kurege.

PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp