Home Labarai Dan takarar Jam’iyyar LP a zauren majalisar Jihar legas bai ji rauni...

Dan takarar Jam’iyyar LP a zauren majalisar Jihar legas bai ji rauni ba, Bincike PRNigeria

Wani bincike da jaridar PRNigeria ta gudanar ya tabbatar da cewa Dan takarar jam’iyyar Labour Party na mazabar Surulere a zauren majalisar jihar Legas, Olumide Oworu, bai ji ciwo ba a zaben daya gabata ranar asabar.

Idan za’a iya tunawa an ta yada wani hoto a shafin Facebook na Oworu da yake nuna yadda yake zubar da jini a yanar gizo yana mai bayyana cewa an kai masa hari shi da tawagar sa abinda ya haddasa masa jikka a yayin zaben.

Haka kuma an ta yada hotunan a kafafen sada zumunta na zamani ciki har da shafin WhatsApp

amma PRNigeria tayi amfani da manhajar binciken hoto ta “reverse image search” kan hoton na Oworu.

Sakamakon ya nuna cewa Oworu da kan ne y afara wallafa hoton da jini a jikin sa a shafukan sada zumunta tun a watan Oktoban shekarar 2022, mai taken “Alagbado John Wick #OntheEdge,”

Haka kuma wani sakamako ya nuna makamancin hoton na dankarar majalisar jihar karkashin inuwar jam’iyyar LP a shafin Instagram na fitacciyar mai yin kwalliya, Carina Ojoko.

PRNigeria ta gano cewa wannan hoton an samo shi ne a cikin wani Shirin wasan kwakwayo mai suna “ On the Edge” bashi da hadi da harin kwanannan da aka ce an kaiwai dan takarar.

Dan haka dangane da binciken da PRNigeria ta gunadar, wannan hoton Olumide Oworu ya fito ne daga wani shiri na “On the Edge,” ba a lokacin harin aka samo shi ba.

Wannan ya sanya PRNigeria ta bayyana labarin matsayin na karlya da kanzon kurege.

PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp