Home Labarai A gurfanar da wadanda suka aikata laifin zabe-Amurka

A gurfanar da wadanda suka aikata laifin zabe-Amurka

Amurka ta yi kira ga hukumomin Najeriya su tabbatar, sun gurfanar da mutanen da aka samu da hannu, ko waɗanda suka ba da umarnin a razana masu zaɓe ko suka daƙile harkar zaɓen gwamnoni a ƙasar.

Cikin wani rahoto da Ofishin jakadancin Amurka a Nijeriya ya fitar ta ce Amurka ta damu matuƙa kan aika-aikar da aka yi wa masu zaɓe ta hanyar razanarwa da daƙile yin zaɓe a jihohi irinsu Kano da Lagos.

Amurka na wannan kira ne a matsayin wani martani ga zaɓen ranar Asabar da ta wuce na gwamnoni da ‘yan majalisun dokokin jihohin ƙasa

Haka kuma Amurkan ta ce ita ma za ta yi nazari a kan dukkan matakan ladabtarwa da take da su, ciki har da ƙarin hana bizar shiga ƙasarta ga mutanen da aka yi imani suna da alhaki, ko an haɗa baki da su wajen yin zagon ƙasa ga tsarin dimokraɗiyyar Nijeriya.

Ofishin jakadancin Amurka a Nijeriya ya ce jami’an diflomasiyyar Amurka da suka sa-ido kan zaɓuka a Lagos da sauran wurare sun ga irin waɗannan kura-kurai da idanuwansu.

Sanarwar ta ce amfani da kalaman ƙabilanci a lokacin zaɓen gwamnan Lagos, musamman abin damuwa ne.

Ta yaba wa duk ‘yan siyasar Nijeriya da shugabannin addinai da na al’umma da matasa da ‘yan ƙasar, waɗanda suka zaɓi bijire wa waccar hanya, kuma suka nuna adawa a kan irin waɗannan kalamai na ta da hankali da tunzura rikici, abin da ke tabbatar da ƙudurin ‘yan ƙasar wajen mutunta tsarin dimokraɗiyya.

Sanarwar ta ce bayan zaɓukan shugaban ƙasa na 25 ga watan jiya, Amurka ta bi sahun masu sa-ido na ƙasashen waje, wajen yin kira ga hukumar zaɓe ta gyara kura-kuren da aka samu a tsare-tsaren yin zaɓe da kuma amfani da na’urori.

Kuma ga alama zaɓukan da suka wuce, sun nuna an samu gagarumin ci gaba, don kuwa akasari an buɗe rumfunan zaɓe a kan lokaci kuma an ga sakamakon zaɓe da yawa a shafin latroni da ke nuna sakamakon da aka wallafa a kan lokaci.

Sanarwar ta sake yin kira ga duk masu ƙorafe-ƙorafe game da zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisun dokokin jiha, su bi kadi ta hanyoyin da doka ta tanada, waɗanda kuma lallai ba za a yi musu katsalandan ba.

Sanarwar ta sake yin kira ga al’ummar Nijeriya su haɗa kai wajen aiki tare kamar yadda suka shiga aka dama da su a zaɓen sabbin shugabanni kuma su ci gaba da ƙoƙari wajen ƙarfafa tsarin dimokraɗiyyar ƙasar mai cike da kuzari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp