Home Labarai Buhari ya ƙi sanya hannu kan dokar da ta bai wa majalisa...

Buhari ya ƙi sanya hannu kan dokar da ta bai wa majalisa damar gayyatar shugaban ƙasa

Shugaban majalisar dattawan Najeriya Sanata Ahmad Lawan, ya ce majalisar za ta sake nazarin sauran dokoki 19 da majalisar ta gyara wa fuska, waɗanda kuma shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya ƙi sanya wa hannu.

Sanata Lawan ya bayyana haka a lokacin zaman majalisar na ranar Talata.

A cikin watan Janairun da ya gabata ne majalisar ta aike wa shugaba Buhari wasu dokoki 35 da majalisar ta yi wa gyaran fuska, domin amincewa da su.

To sai dai a makon da ya gabata shugaban ƙasar ya amince da dokoki 16 cikin 35 din da ta aike masa.

Sanata Lawan ya ce ɗaya daga cikin sabbin dokokin da shugaban ƙasar ya sanya wa hannu ita ce dokar da ta tanadi samar da ‘yancin gashin kai a ɓangaren kashe kuɗade ga majalisun dokokin jiha da ɓangaren shari’a.

To sai dai ɗaya daga cikin dokoki dokoki 19 da shugaban ƙasar ya ƙi sanya hannu a kai har da dokar da ta bai wa majalisar dokoki ta ƙasa da majalisun dokokin jihohi damar gayyatar shugaban ƙasa ko gwamna, domin yin bayani kan wasu abubuwan da majalisar dokoki ta ƙasa ko majalisun dokokin jihohi ke da damar aiwatarwa.

Da kuma dokar da aka yi wa gyaran fuska wadda ta tanadi tilasta wa shugaban ƙasa ko gwamna bin umarni ko yin biyayya ga gayyatar da majalisa ta yi masa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp