Home Labarai Sojojin saman Nijeriya sun hallaka ‘yan boko haram 12 a Sambisa

Sojojin saman Nijeriya sun hallaka ‘yan boko haram 12 a Sambisa

Harin rundunar sojin saman Nijeriya yayi sanadiyyar tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda masu tayar da kayar baya a dajin Sambisa da ke yankin tafkin chadi tare da hallaka mayakan 12.

Ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai da bayanai na rundunar sojin saman Nijeriya Air Vice Marshal Edward Gabkwet ya fita mai dauke da kwanan watan 7 ga watan Janairu 2024.

Sanarwar ta ce a kokarin rundunar sojin na kakkabe matsalolin rashin tsaron a yankin arewa maso gabashin kasar, rundunar na cigaba da samun nasara, in da a ranar 5 ga watan janairun wannan shekara rundunar ta sami nasara a Parisu bayan wani bayanan sirri da ta samu na yadda ‘yan ta’adda ke karakaina da makamai da alburusai a yankin.

Parisu wani yanki ne dake kusa da dajin sambisa, wanda ‘yan ta’adda suka taba mamaye shi, sai dai daga bisani sojojin Nijeriya suka, harin da ya yi sanadiyya mutuwar mayakn da dama tare da kwace maboyar ta su.

Haka kuma rahotannin sun bayyana cewa ‘yan ta’adda 12 aka hallaka yayin harin dakarun ta sama, tare da tarwatse maboyar su, harin kuma ya dakile yunkurin ‘yan bindigar na kai hari kan dakarun sojojin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp