Home General Kotu ta dakatar da Dawo da Sunusi Lamido sarautar Kano

Kotu ta dakatar da Dawo da Sunusi Lamido sarautar Kano

Babbar kotun tarayya a jihar kano ta bada umarnin dawo da sarkin Kano Muhammadu Sunusi kan karagar mulkin masarautar jihar.

Mai shari’a AM liman ne ya bayar da umarnin gaggauta dakatarwa ga gwamnatin jihar, bayan bayan wata kara da sarkin Dawaki Babba, Aminu Babba dan Agundi ya shigar gaban kotun.

Alhaji Aminu Babba Dan Agundi ya yi karar Rukunonin guda 8 da suka haɗar da Gwamnatin jihar kano, Majalisar dokokin jihar, Kakakin Majalisar dokokin jihar, Kwamishinan Shari’ar na Kano, Kwamishinan yan sandan jihar, Babban sufeton yan sandan Nigeria , Civil Defense, da kuma hukumar DSS.

Idan dai za’a iya tunawa Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautun jihar ta 2024 bayan da majalisar dokoki ta soke dukkan masarautun jihar biyar da aka ƙirƙira a shekarar 2019.

Jim kaɗan bayan rattaba hannu a kan dokar, gwamnan ya sanar da naɗa Khalifa Muhammadu Sanusi II a matsayin sabon Sarkin Kano na 16, bayan ya sauke Aminu Ado Bayero daga kan kujerar.

Matakin kuma ya nuna cewa an soke masarautun Gaya da Bichi da Ƙaraye da kuma na Rano.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp