Home DUNIYA Gwamnatin Kano za ta kammala gina cibiyoyin koyar da sana’o’i

Gwamnatin Kano za ta kammala gina cibiyoyin koyar da sana’o’i

Gwamnatin jihar Kano ta yi alƙawarin kammala aikin gyara dukkannin cibiyoyin koyar da sana,oin dogaro da Kai da kuma kirkire-kirkire Wanda tsohon Gwamna Rabi’u Musa kwankwaso ya Samar tun a shekarar 2011 a daukacin ƙananan hukumomi 44 da ke Kano.

Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan yayin bikin ranar baje kolin fasahar matasa ta duniya da cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote dake ƙaramar hukumar Dawakin kudu haɗin gwiwa da hukumar kula da ilimin ƙananan yara ta duniya UNESCO ta shirya.

Gwamnan ya ce yin riko da sana’o’in hannu zai taimaka wajen habaka tattalin arziki da Kuma samawa Matasa aikin yi.

Abba Kabir ya yi alkawarin samawa cibiyar da gidajen kwanan dalibai da biya musu kudin karatu da daukar nauyin kai su makaranta a kullum da kuma kulawa da walwalarsu.

Da ya ke jawabi a wajen taron karamin ministan ma’aikatar ci-gaban matasa Mista Ayodele Olawode ya yaba da harkokin cibiyar, inda ya ce ma’aikatar sa ta fito da wani shirin ilimantar da matasa miliyan 7 sana’o’in dogaro da kai.

Shugaban Hukumar UNESCO a Nijeriya Abdulrahman Diyalo ya ce za su yi haɗin gwiwa da gwamnatin kano da cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote domin koyar da dubban matasa sana’o’in dogaro da kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp