Gwamnatin Kano za ta kammala gina cibiyoyin koyar da sana’o’i

Gwamnatin jihar Kano ta yi alƙawarin kammala aikin gyara dukkannin cibiyoyin koyar da sana,oin dogaro da Kai da kuma kirkire-kirkire Wanda tsohon Gwamna Rabi’u Musa kwankwaso ya Samar tun a shekarar 2011 a daukacin ƙananan hukumomi 44 da ke Kano.

Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan yayin bikin ranar baje kolin fasahar matasa ta duniya da cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote dake ƙaramar hukumar Dawakin kudu haɗin gwiwa da hukumar kula da ilimin ƙananan yara ta duniya UNESCO ta shirya.

Gwamnan ya ce yin riko da sana’o’in hannu zai taimaka wajen habaka tattalin arziki da Kuma samawa Matasa aikin yi.

Abba Kabir ya yi alkawarin samawa cibiyar da gidajen kwanan dalibai da biya musu kudin karatu da daukar nauyin kai su makaranta a kullum da kuma kulawa da walwalarsu.

Da ya ke jawabi a wajen taron karamin ministan ma’aikatar ci-gaban matasa Mista Ayodele Olawode ya yaba da harkokin cibiyar, inda ya ce ma’aikatar sa ta fito da wani shirin ilimantar da matasa miliyan 7 sana’o’in dogaro da kai.

Shugaban Hukumar UNESCO a Nijeriya Abdulrahman Diyalo ya ce za su yi haɗin gwiwa da gwamnatin kano da cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote domin koyar da dubban matasa sana’o’in dogaro da kai.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 13 hours 37 minutes 30 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 15 hours 18 minutes 55 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com