Home General Sojojin Nijeriya sun tura sako ga masu Shirin gudanar da Zanga –...

Sojojin Nijeriya sun tura sako ga masu Shirin gudanar da Zanga – Zanga

Shalkwatar tsaron Najeriya ta gargaɗi masu shirin shirya zanga-zanga tsadar rayuwa a faɗin ƙasar da su guji jefa ƙasar cikin ruɗani.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran ma’aikatar tsaron ƙasar, Manjo Janar Edward Buba ya fitar, inda ya ce duk da cewa ‘yan ƙasar na da ‘yancin gudanar da zanga-zangar, rundunar tsaron ƙasar ba za ta lamunci tayar da fitina a ƙasar ba.

Ya ce rundunar ta fahimci masu shirya zanga-zangar na yunƙurin kwaikwayar abin da ya faru a Kenya, inda zanga-zangar ta rikiɗe zuwa tashin hankali.

”Koda yake ‘yan Najeriya na da ‘yancin bayyana abin da ke damunsu, sojoji ba za su lamunci duk wani abu da zai iya janyo tashin hankali a ƙasar nan da sunan zanga-zanga ba”, in ji sanarwar.

Ya ƙara da cewa, sojojin sun bankaɗo shirin wasu ‘ɓata-gari’ da ke ƙoƙarin amfani da zanga-zangar wajen farmakar ‘yan ƙasar da ba su ji ba su gani ba.

“Yayin da ‘yan ƙasa ke da ‘yancin gudanar da zanga-zangar lumana, ba su da hujjar shirya wani abu da ka iya tayar da tarzoma ko aikata laifuka”, in ji Manjo Janar Buba.

“Mun dai ga abin da ya faru a Kenya, inda wasu ɓata-gari suka mayar da zanga-zangar lumana zuwa tashin hankali, wanda kuma aka kasa magancewa”, in ji shi.

Ya ce sojojin ƙasar sun sha zuwa ayyukan wanzar da zaman lafiya a ƙasashe makwabta musamman ƙarƙashin shirin samar da tsaro na yammacin Afirka, ECOMOG, kuma sun san yadda al’umomin ƙasashen ke faɗawa cikin mawuyacin hali sakamakon tashe-tashen hankulan, don haka ba su so hakan ta faru a Najeriya ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp