Home WASANNI Kano Pillars ta gabatar da sabbin ‘Yan wasa 12

Kano Pillars ta gabatar da sabbin ‘Yan wasa 12

Tawagar Kano Pillars FC, wacce ta lashe gasar Nigeria Premier Football League, NPFL, sau hudu, ta sanar da sababbin ‘yan wasan da ta dauka a hukumance gabanin kakar wasanni ta 2024/25.

An gudanar da taron bikin gabatar da sabbin ‘yan wasan a filin wasa na Sani Abacha a ranar Laraba, 4 ga Satumba, 2024, tare da halartar Shugaban tawagar, Alhaji Ali Muhammad Na Yara Mai Samba, gami da wasu daga cikin mambobin kwamitin gudanarwa.

A shirye-shiryen da take yi don sabuwar kakar wasannin, tawagar ta dauki sabbin ‘yan wasa guda goma sha biyu, tare da mai da hankali kan wasu muhimman wurare don kara karfin tawagar.

Wannan shiri ya nuna kudirin Kano Pillars FC na dawo da matsayinta na babbar tawagar ƙwallon kafar Nijeriya.

Sabbin ‘yan wasan sun hada da masu tsaron gida guda uku, wasu masu tsaron baya, ‘yan wasan tsakiya, da ‘yan wasan gaba, wadanda suka hada da ‘yan wasan cikin gida da kuma na kasashen waje.

Bugu da kari baya da sababbin ‘yan wasan da aka dauka, tawagar ta ci gaba da rike ‘yan wasa ashirin daga kakar wasannin da ta gabata, wanda hakan zai haifar da taka leda mai kyau ga tawagar.

Kano Pillars FC za ta fara buga gasar NPFL ta 2024/25 a ranar 8 ga Satumba, 2024, inda za ta rika buga wasanninta na gida a filin wasa na Muhammad Dikko da ke Katsina a matsayin wucin gadi, saboda gyare-gyaren da ake yi a filin wasa na Sani Abacha.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp