Home WASANNI Kano Pillars ta gabatar da sabbin ‘Yan wasa 12

Kano Pillars ta gabatar da sabbin ‘Yan wasa 12

Tawagar Kano Pillars FC, wacce ta lashe gasar Nigeria Premier Football League, NPFL, sau hudu, ta sanar da sababbin ‘yan wasan da ta dauka a hukumance gabanin kakar wasanni ta 2024/25.

An gudanar da taron bikin gabatar da sabbin ‘yan wasan a filin wasa na Sani Abacha a ranar Laraba, 4 ga Satumba, 2024, tare da halartar Shugaban tawagar, Alhaji Ali Muhammad Na Yara Mai Samba, gami da wasu daga cikin mambobin kwamitin gudanarwa.

A shirye-shiryen da take yi don sabuwar kakar wasannin, tawagar ta dauki sabbin ‘yan wasa guda goma sha biyu, tare da mai da hankali kan wasu muhimman wurare don kara karfin tawagar.

Wannan shiri ya nuna kudirin Kano Pillars FC na dawo da matsayinta na babbar tawagar ƙwallon kafar Nijeriya.

Sabbin ‘yan wasan sun hada da masu tsaron gida guda uku, wasu masu tsaron baya, ‘yan wasan tsakiya, da ‘yan wasan gaba, wadanda suka hada da ‘yan wasan cikin gida da kuma na kasashen waje.

Bugu da kari baya da sababbin ‘yan wasan da aka dauka, tawagar ta ci gaba da rike ‘yan wasa ashirin daga kakar wasannin da ta gabata, wanda hakan zai haifar da taka leda mai kyau ga tawagar.

Kano Pillars FC za ta fara buga gasar NPFL ta 2024/25 a ranar 8 ga Satumba, 2024, inda za ta rika buga wasanninta na gida a filin wasa na Muhammad Dikko da ke Katsina a matsayin wucin gadi, saboda gyare-gyaren da ake yi a filin wasa na Sani Abacha.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp