Home General Duk wanda ya ci zaɓen jihar Edo a ba shi – Tinubu

Duk wanda ya ci zaɓen jihar Edo a ba shi – Tinubu

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi kira da dukkan masu ruwa da tsaki a jihar Edo da su tabbatar an martaba ƙuri’a da zaɓin mutanen Edo a zaɓen da za a yi gobe.

Tinubu ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a ta hannun mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga.

“Shugaba Tinubu yana kira ga ƴan takara da jam’iyyu da magoya baya da su martaba tsarin dimokuraɗiyya da zaɓin mutane. Ya yi ammanar cewa mutanen za su yi zaɓi wanda suka ga ya dace da shugabantarsu,” kamar yadda sanarwar ta nuna.

Da yake kira ga Hukumar INEC da jami’an tsaro su kasance na kowa, Shugaba Tinubu ya ce dole kowane ɓangare ya gudanar da harkokinsa cikin lumana.

Tinubu ya nanata cewa domokuraɗiyya na cigaba ne idan akwai fahimtar juna da hakuri da kuma girmama tsarin ƙasa, inda ya ƙara da cewa INEC ta ɗauki alwashin gudanar da zaɓe sahihi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp