Home General Duk wanda ya ci zaɓen jihar Edo a ba shi – Tinubu

Duk wanda ya ci zaɓen jihar Edo a ba shi – Tinubu

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi kira da dukkan masu ruwa da tsaki a jihar Edo da su tabbatar an martaba ƙuri’a da zaɓin mutanen Edo a zaɓen da za a yi gobe.

Tinubu ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a ta hannun mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga.

“Shugaba Tinubu yana kira ga ƴan takara da jam’iyyu da magoya baya da su martaba tsarin dimokuraɗiyya da zaɓin mutane. Ya yi ammanar cewa mutanen za su yi zaɓi wanda suka ga ya dace da shugabantarsu,” kamar yadda sanarwar ta nuna.

Da yake kira ga Hukumar INEC da jami’an tsaro su kasance na kowa, Shugaba Tinubu ya ce dole kowane ɓangare ya gudanar da harkokinsa cikin lumana.

Tinubu ya nanata cewa domokuraɗiyya na cigaba ne idan akwai fahimtar juna da hakuri da kuma girmama tsarin ƙasa, inda ya ƙara da cewa INEC ta ɗauki alwashin gudanar da zaɓe sahihi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp