Home General Gwamnatin Kano ta kulla alaka da kasar India

Gwamnatin Kano ta kulla alaka da kasar India

Gwamnatin jihar Kano ta kulla alakar inganta tattalin arziki da ilimi da kasar India, a wani bangare na yunkurinta na inganta kyakkyawar alaka.

Wannan na cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labaran Gwamnan jihar Kano Sunusi bature Dawakin Tofa ya aikewa PRNigeria a ranar juma’a.

Inda ta ce gwamnan jihar Kano Alhaji Abba kabir Yusuf, ya bayyana hakan ne a yayin da yake karbar bakuncin jakadan kasar ta india Excellency Shri G. Balasubramanian a fadar gwamnatin jihar.

Abba kabir ya bayyana cewa akwai kyakkyawar alaka tsakanin kasar India da jihar kano musamman a fannin Ilimi, Lafiya, Noma, kasuwanci da kuma kere-kere, wadda take bukatar aka mata karfi domin amfanin kasar ta India da kuma jihar Kano.

Ya kuma kara da cewa gwamnatin kano zata cigaba da hadin gwiwa da india domin kamala tashoshinta na samar da hasken wutar lantarki guda biyu da suka hadar da Tiga da Challawa, domin habaka kamfanoni da kuma cigaban tattalin arziki.

Tun da fari dai da yake jawabi wakilin kasar Indian Excellency Shri G. Balasubramanian ya yaba da kokarin gwamnan bisa samar da ayyukan cigaba da zai taimakawa al’ummar jihar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp