Home General Ambaliya: mutum 25 sun rasu, gidaje 312,000 sun rushe a Kebbi

Ambaliya: mutum 25 sun rasu, gidaje 312,000 sun rushe a Kebbi

Gwamnatin Kebbi ta ce aƙalla an yi asarar rayukan mutane 29 da gidaje 321,000 da gonaki 858,000 sanadiyyar ambaliyar ruwa a ƙananan hukumomi 16 daga cikin 21 na jihar.

Kwamishinan Labarai, Yakubu Ahmed Birnin Kebbi ne bayyana hakan a ranar Juma’a a yayin zantawa da manema labarai a cibiyar manema labarai da ke Birnin Kebbi.

Ya ce, idan ba ɗauki mataki a yankunan da abin ya shafa ba, wanda suka rasa shinkafa da Masara da dawa da sauran amfanin gona da ambaliyar ta lalata za a iya samun ƙarancin abinci a jihar da kasar.

Ya ce, kafin gargaɗin da Hukumar Hasashen Yanayi NIMET ta yi, jihar ta fuskanci ibtila’i mai tsanani sakamakon ambaliya a ƙananan hukumomi 16 na jihar a dalilin ruwan da aka sako daga Madatsar Ruwa ta Goronyo da kuma magudanar ruwa a kogin Rima da kogin kaa da ke kwararo tun daga Kogin Neja.

Kwamishinan ya ce duk da matakan da gwamnatin ta ɗauka har yanzu jihar na fama da ambaliyar ruwa a ƙananan hukumominta 16.

“Kananan hukumomi 5 daga cikin 21 na jihar ne kaɗai abin bai shafa ba. Ambaliyar ta lalata gonaki, gadoji da dubban gidaje.

“Game da adadin wadanda suka mutu, mun rasa mutane bakwai a Shanga, takwas a Maiyama, biyar a Kalgo. Kazalika, an rasa mutum bakwai a Jega, biyu kuma a Birnin Kebbi,” in ji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp