Home General Ambaliya: mutum 25 sun rasu, gidaje 312,000 sun rushe a Kebbi

Ambaliya: mutum 25 sun rasu, gidaje 312,000 sun rushe a Kebbi

Gwamnatin Kebbi ta ce aƙalla an yi asarar rayukan mutane 29 da gidaje 321,000 da gonaki 858,000 sanadiyyar ambaliyar ruwa a ƙananan hukumomi 16 daga cikin 21 na jihar.

Kwamishinan Labarai, Yakubu Ahmed Birnin Kebbi ne bayyana hakan a ranar Juma’a a yayin zantawa da manema labarai a cibiyar manema labarai da ke Birnin Kebbi.

Ya ce, idan ba ɗauki mataki a yankunan da abin ya shafa ba, wanda suka rasa shinkafa da Masara da dawa da sauran amfanin gona da ambaliyar ta lalata za a iya samun ƙarancin abinci a jihar da kasar.

Ya ce, kafin gargaɗin da Hukumar Hasashen Yanayi NIMET ta yi, jihar ta fuskanci ibtila’i mai tsanani sakamakon ambaliya a ƙananan hukumomi 16 na jihar a dalilin ruwan da aka sako daga Madatsar Ruwa ta Goronyo da kuma magudanar ruwa a kogin Rima da kogin kaa da ke kwararo tun daga Kogin Neja.

Kwamishinan ya ce duk da matakan da gwamnatin ta ɗauka har yanzu jihar na fama da ambaliyar ruwa a ƙananan hukumominta 16.

“Kananan hukumomi 5 daga cikin 21 na jihar ne kaɗai abin bai shafa ba. Ambaliyar ta lalata gonaki, gadoji da dubban gidaje.

“Game da adadin wadanda suka mutu, mun rasa mutane bakwai a Shanga, takwas a Maiyama, biyar a Kalgo. Kazalika, an rasa mutum bakwai a Jega, biyu kuma a Birnin Kebbi,” in ji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp