Home General Gwamnatin Kano ta kulla alaka da kasar India

Gwamnatin Kano ta kulla alaka da kasar India

Gwamnatin jihar Kano ta kulla alakar inganta tattalin arziki da ilimi da kasar India, a wani bangare na yunkurinta na inganta kyakkyawar alaka.

Wannan na cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labaran Gwamnan jihar Kano Sunusi bature Dawakin Tofa ya aikewa PRNigeria a ranar juma’a.

Inda ta ce gwamnan jihar Kano Alhaji Abba kabir Yusuf, ya bayyana hakan ne a yayin da yake karbar bakuncin jakadan kasar ta india Excellency Shri G. Balasubramanian a fadar gwamnatin jihar.

Abba kabir ya bayyana cewa akwai kyakkyawar alaka tsakanin kasar India da jihar kano musamman a fannin Ilimi, Lafiya, Noma, kasuwanci da kuma kere-kere, wadda take bukatar aka mata karfi domin amfanin kasar ta India da kuma jihar Kano.

Ya kuma kara da cewa gwamnatin kano zata cigaba da hadin gwiwa da india domin kamala tashoshinta na samar da hasken wutar lantarki guda biyu da suka hadar da Tiga da Challawa, domin habaka kamfanoni da kuma cigaban tattalin arziki.

Tun da fari dai da yake jawabi wakilin kasar Indian Excellency Shri G. Balasubramanian ya yaba da kokarin gwamnan bisa samar da ayyukan cigaba da zai taimakawa al’ummar jihar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp