Home General Gwamnatin Kano ta kulla alaka da kasar India

Gwamnatin Kano ta kulla alaka da kasar India

Gwamnatin jihar Kano ta kulla alakar inganta tattalin arziki da ilimi da kasar India, a wani bangare na yunkurinta na inganta kyakkyawar alaka.

Wannan na cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labaran Gwamnan jihar Kano Sunusi bature Dawakin Tofa ya aikewa PRNigeria a ranar juma’a.

Inda ta ce gwamnan jihar Kano Alhaji Abba kabir Yusuf, ya bayyana hakan ne a yayin da yake karbar bakuncin jakadan kasar ta india Excellency Shri G. Balasubramanian a fadar gwamnatin jihar.

Abba kabir ya bayyana cewa akwai kyakkyawar alaka tsakanin kasar India da jihar kano musamman a fannin Ilimi, Lafiya, Noma, kasuwanci da kuma kere-kere, wadda take bukatar aka mata karfi domin amfanin kasar ta India da kuma jihar Kano.

Ya kuma kara da cewa gwamnatin kano zata cigaba da hadin gwiwa da india domin kamala tashoshinta na samar da hasken wutar lantarki guda biyu da suka hadar da Tiga da Challawa, domin habaka kamfanoni da kuma cigaban tattalin arziki.

Tun da fari dai da yake jawabi wakilin kasar Indian Excellency Shri G. Balasubramanian ya yaba da kokarin gwamnan bisa samar da ayyukan cigaba da zai taimakawa al’ummar jihar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp