Home General Gwamnatin Kano ta kulla alaka da kasar India

Gwamnatin Kano ta kulla alaka da kasar India

Gwamnatin jihar Kano ta kulla alakar inganta tattalin arziki da ilimi da kasar India, a wani bangare na yunkurinta na inganta kyakkyawar alaka.

Wannan na cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labaran Gwamnan jihar Kano Sunusi bature Dawakin Tofa ya aikewa PRNigeria a ranar juma’a.

Inda ta ce gwamnan jihar Kano Alhaji Abba kabir Yusuf, ya bayyana hakan ne a yayin da yake karbar bakuncin jakadan kasar ta india Excellency Shri G. Balasubramanian a fadar gwamnatin jihar.

Abba kabir ya bayyana cewa akwai kyakkyawar alaka tsakanin kasar India da jihar kano musamman a fannin Ilimi, Lafiya, Noma, kasuwanci da kuma kere-kere, wadda take bukatar aka mata karfi domin amfanin kasar ta India da kuma jihar Kano.

Ya kuma kara da cewa gwamnatin kano zata cigaba da hadin gwiwa da india domin kamala tashoshinta na samar da hasken wutar lantarki guda biyu da suka hadar da Tiga da Challawa, domin habaka kamfanoni da kuma cigaban tattalin arziki.

Tun da fari dai da yake jawabi wakilin kasar Indian Excellency Shri G. Balasubramanian ya yaba da kokarin gwamnan bisa samar da ayyukan cigaba da zai taimakawa al’ummar jihar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp