Home General EFCC ta kama tsohon gwamnan Taraba kan badakalar Biliyan 27

EFCC ta kama tsohon gwamnan Taraba kan badakalar Biliyan 27

Hukumar dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin Nijeriya zagon kasa ta EFCC ta tsare tsohon Gwamnan jihar Taraba Darius Ishaku bisa zargin halasta kudin haram ya zuka kai naira biliyan 27 a lokacin da yake bisa karagar mulkin jihar

EFCC ta na tuhuwar tsohon Gwamnan  wasu tuhume-tuhume guda goma sha biyar dake da nasaba da almundahana da dukiyar al’umma

Rahotanni sun bayyana cewa, a wannan Juma’a ne jami’an EFCC suka yi dirar mikiya a gidan tsohon gwamnan da ke Abuja wanda wa’adinsa ya ƙare a shekarar 2023 bayan shafe tsawon shekaru takwas a kan madafun iko.

EFCC ta ce gwamnan yana hannun hukumar inda ake titsiye shi.

Hukumar ta EFCC ta kammala tattara aƙalla tuhume-tuhume 15 da ake zargin tsohon gwamnan kuma nan ba da jimawa ba zai gurfana a gaban kuliya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp