Home General Tinubu ya rantsar da Kudirat Kekere-Ekun babbar mai shari’a ta Najeriya

Tinubu ya rantsar da Kudirat Kekere-Ekun babbar mai shari’a ta Najeriya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya rantsar da Mai Shari’a Kudirat Olatokunbo Kekere-Ekun domin kama aiki a matsayin babbar mai shari’a ta ƙasa a ranar Litinin bayan Majalisar Dattawa ta amince da naɗin nata.

Ita ce mace ta biyu da take riƙe muƙamin a tarihi, kamar yadda wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasa ta bayyana.

An yi bikin rantsuwar ne a gaban tsofaffin manyan alƙalai huɗu, ciki har da mace ta farko da ta riƙe muƙamin Mariam Aloma Mukhtar.

“Fannin shari’a babban ginshiƙi ne da ke tallafe da tsarin dimokuɗaiyarmu, kuma tsawon shekaru fannin shari’ar Najeriya ya sha nuna tasirinsa na mai shiga tsakani domin tabbatar kowa ya bi doka,” a cewar Shugaba Tinubu yayin taron.

“Matsayinki na zama wuri na ƙarshe da talaka zai samu adalci yana da muhimmanci wajen saka wa mutane ƙwarin gwiwa kan dimokuraɗiyya,” in ji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp