Home General Rundunar ƴansanda ta kama mutane 89 da ake zargi da aikata laifuka...

Rundunar ƴansanda ta kama mutane 89 da ake zargi da aikata laifuka a Kano

Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta kama mutane 89 bisa zargin aikata laifuka daban-daban, wannan na matsayi kokarin hukumar na magance ayyukan bata gari a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya,

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Salman Dogo ne ya bayyana hakan yayin da yake yiwa manema labarai jawabi a shelkwatar rundunar dake Bompai, Kano a ranar Litinin.

Dogo ya ce laifukan da mutanen suka aikata sun hada da garkuwa da mutane don neman kudin fansa da fashi da makami da ta’ammali da miyagun kwayoyi.

Ya ce, an yi kamen ne a wurare daban daban na jihar, daga ranar 12 ga watan Satumba zuwa yau inda ya kara da cewa an mika mutane 53 da ake zargi gaban kotu a yayin da 36 ake kan bincike a kansu.

Kwamishinan wanda ya samu wakilcin SP, Abdullahi Haruna Kiyawa, mai magana da yawun rundunar, ya ce an kwato makamai masu hatsari daga wajen wadanda ake zargin da suka hada da bindiga da adda da wukake.

Sannan ya ce rundunar za ta ci gaba da aiwatar da aikin ta kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

“A don haka, rundunar ‘yansanda zata ci gaba da sauke nauyin dake kanta kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada”, inji Kwamishinan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp