Home AFIRKA DalilinTanzania na dakatar da jaridar The Citizen a kasar

DalilinTanzania na dakatar da jaridar The Citizen a kasar

Gwamnatin Tanzania ta dakatar da wata jarida da ke kan gaba a ƙasar da ake wallafawa a shafin internet, bayan ta wallafa hotunan da ke alakanta shugabar ƙasar, Samia Suluhu Hassan da sace-sace da kuma kashe kashen ƴan adawa da aka yi a baya-bayan nan.

Ɗaya daga cikin hotunan bidiyo da jaridar The Citizen ta wallafa  ya nuna shugaba Samia Suluhu Hassan zaune tana kallon bidiyon cin zarafin da aka yi wa ƴan adawa haɗe da wasu da ba su ji ba basu gani ba.

Gabanin faruwar lamarin shugabar ƙasar ta fuskanci caccaka daga ciki da wajen Tanzania game da zarge-zargen da ake yi wa jami’an tsaron ƙasar da alhakin yin garkuwa tare da kashe wasu daga cikin jiga jigan jamiyyar adawa na ƙasar.

Tuni dai jaridar ta cire tallace-tallacen da ta wallafa, kana ta fitar da sanarwar da ke cewa manufarsu ita ce bayyana damuwar allummar ƙasar a game da matsalolin tsaro.

A ranar Laraba ne The Citizen da ke kan gaba daga cikin jaridun da ake walafawa da harshen Turanci a Tanzania ta fitar da sanarwar dakatar da ayyukanta na tsawon kwanaki 30 da hukumar da ke kula da harkokin sadarwa ta  Tanzaniya ta yi.

Tun a cikin watan Agustan da ya gabata ne dai, gwamnatin Samia Suluhu Hassan ta haramta manyan gangami biyu da jam’iyyar Chadema ta ƙaddamar, sannan ta sanar da batun tsare shugabannin jam’iyyar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp