Home AFIRKA DalilinTanzania na dakatar da jaridar The Citizen a kasar

DalilinTanzania na dakatar da jaridar The Citizen a kasar

Gwamnatin Tanzania ta dakatar da wata jarida da ke kan gaba a ƙasar da ake wallafawa a shafin internet, bayan ta wallafa hotunan da ke alakanta shugabar ƙasar, Samia Suluhu Hassan da sace-sace da kuma kashe kashen ƴan adawa da aka yi a baya-bayan nan.

Ɗaya daga cikin hotunan bidiyo da jaridar The Citizen ta wallafa  ya nuna shugaba Samia Suluhu Hassan zaune tana kallon bidiyon cin zarafin da aka yi wa ƴan adawa haɗe da wasu da ba su ji ba basu gani ba.

Gabanin faruwar lamarin shugabar ƙasar ta fuskanci caccaka daga ciki da wajen Tanzania game da zarge-zargen da ake yi wa jami’an tsaron ƙasar da alhakin yin garkuwa tare da kashe wasu daga cikin jiga jigan jamiyyar adawa na ƙasar.

Tuni dai jaridar ta cire tallace-tallacen da ta wallafa, kana ta fitar da sanarwar da ke cewa manufarsu ita ce bayyana damuwar allummar ƙasar a game da matsalolin tsaro.

A ranar Laraba ne The Citizen da ke kan gaba daga cikin jaridun da ake walafawa da harshen Turanci a Tanzania ta fitar da sanarwar dakatar da ayyukanta na tsawon kwanaki 30 da hukumar da ke kula da harkokin sadarwa ta  Tanzaniya ta yi.

Tun a cikin watan Agustan da ya gabata ne dai, gwamnatin Samia Suluhu Hassan ta haramta manyan gangami biyu da jam’iyyar Chadema ta ƙaddamar, sannan ta sanar da batun tsare shugabannin jam’iyyar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp