Home General Kotu ta dakatar da hukumar VIO daga cin tarar masu ababen hawa...

Kotu ta dakatar da hukumar VIO daga cin tarar masu ababen hawa a Najeriya

Babbar kotun tarayya a Najeriya da ke zamanta a Abuja, ta haramtawa Hukumar Kula da Lafiyar Ababen Hawa ta VIO, ta daina kamawa da kwacewa ko kuma cin tarar masu ababen hawa.

Haka kotun ta umarci jami’an hukumar na VIO su daina tsaida masu ababen hawa akan hanyoyin ƙasar.

Mai shari’a Evelyn Maha ce dai ta yanke wannan hukuncin, bayan da Abubakar Marshal, mai rajin kare hakkin bil’adama ya shigar da ƙara kan lamarin.

A hukuncin nata ta ce, kotun ta gamsu da hujjojin mai ƙara na cewa babu wata doka da ta baiwa waɗanda ake ƙara hurumin tsaidawa da kamawa da kwacewa ko kuma cin tarar masu ababen hawa a kan hanya.

Mai shari’a Maha ta kuma bada umarnin dakatar da waɗanda ake ƙara, daga tauye haƙƙin ƴan Najeriya na yin zirga-zirga yadda suke suke so ba tare da sahalewar doka ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp