Home Labarai Tinubu ya sallami ministoci biyar cikin kunshin ministocinsa

Tinubu ya sallami ministoci biyar cikin kunshin ministocinsa

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sallami ministoci biyar tare da naɗa wasu sababbi bakwai da kuma sauya wa goma ma’aikatu.

Wata sanarwa da fadar gwamnatin kasar ta fitar a shafinta na X, ta nuna cewa ministocin da aka cire sun hadar da Barr. Uju-Ken Ohanenye; ma’aikatar harkokin mata, Lola Ade-John; ministan harkokin yawon buɗe idanu, Farfesa Tahir Mamman; ministan ilimi, Abdullahi Muhammad Gwarzo; ƙaramin ministan gidaje da raya birane, Dr. Jamila Bio Ibrahim; ministar matasa.

Sai dai shugaba Bola Tinubu ya sauya wasu daga cikin ministocin ma’aikatu da suka hadar da Hon Dr. Yusuf Tanko Sununu; ƙaramin ministan ilimi ya koma ƙaramin ministan jinƙai da rage talauci, Dr. Morufu Olatunji Alausa; ƙaramin ministan lafiya, ya koma ministan ilimi, Barr. Bello Muhammad Goronyo, ƙaramin ministan ruwa da tsafta, ya zama ƙaramin ministan ayyuka, Hon. Abubakar Eshiokpekha Momoh, ministan raya Naija Delta, ya koma ma’aikatar raya yankuna (sabuwa), Uba Maigari Ahmadu, ƙaramin ministan ƙarafa ya koma ƙaramin ministan raya yankuna, Dr. Doris Uzoka-Anite, ministar masana’antu da kasuwanci da zuba jari ta koma ƙaramar ministar kuɗi, Sen. John Owan Enoh, ministan raya wasanni ya koma ƙaramin ministan kasuwanci da zuba jari (masana’antu), Imaan Sulaiman-Ibrahim, ƙaramar ministar harkokin ‘yansanda ta koma ministar mata, Ayodele Olawande, ƙaramin ministan matasa ya koma ministan raya matasa, Dr. Salako Iziaq Adekunle Adeboye, ƙaramin ministan muhalli, ya koma ƙaramin ministan lafiya.

shugaban kasar ya kuma nada sabbin ministocin da suka hadar da Dr Nentawe Yilwatda – Ministan ma’aikatar jinƙai da yaye talauci, Muhamamd Maigari Dingyaɗi – Ministan ƙwadago, Bianca Odinaka Odumegu-Ojukwu – Ƙaramar ministar harkokin waje, Dr Jumoke Oduwale – Ministar ma’aikatar kasuwanci da zuba jari, Idi Mukhtar Maiha – Ma’aikatar kusa da dabbobi, Hon Yusuf Abdullahi Ata – Ƙaramin ministan gidaje da raya birane, Suwaiba Said Ahmad phD – Ministar Ilimi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp