Home Labarai Tinubu ya sallami ministoci biyar cikin kunshin ministocinsa

Tinubu ya sallami ministoci biyar cikin kunshin ministocinsa

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sallami ministoci biyar tare da naɗa wasu sababbi bakwai da kuma sauya wa goma ma’aikatu.

Wata sanarwa da fadar gwamnatin kasar ta fitar a shafinta na X, ta nuna cewa ministocin da aka cire sun hadar da Barr. Uju-Ken Ohanenye; ma’aikatar harkokin mata, Lola Ade-John; ministan harkokin yawon buɗe idanu, Farfesa Tahir Mamman; ministan ilimi, Abdullahi Muhammad Gwarzo; ƙaramin ministan gidaje da raya birane, Dr. Jamila Bio Ibrahim; ministar matasa.

Sai dai shugaba Bola Tinubu ya sauya wasu daga cikin ministocin ma’aikatu da suka hadar da Hon Dr. Yusuf Tanko Sununu; ƙaramin ministan ilimi ya koma ƙaramin ministan jinƙai da rage talauci, Dr. Morufu Olatunji Alausa; ƙaramin ministan lafiya, ya koma ministan ilimi, Barr. Bello Muhammad Goronyo, ƙaramin ministan ruwa da tsafta, ya zama ƙaramin ministan ayyuka, Hon. Abubakar Eshiokpekha Momoh, ministan raya Naija Delta, ya koma ma’aikatar raya yankuna (sabuwa), Uba Maigari Ahmadu, ƙaramin ministan ƙarafa ya koma ƙaramin ministan raya yankuna, Dr. Doris Uzoka-Anite, ministar masana’antu da kasuwanci da zuba jari ta koma ƙaramar ministar kuɗi, Sen. John Owan Enoh, ministan raya wasanni ya koma ƙaramin ministan kasuwanci da zuba jari (masana’antu), Imaan Sulaiman-Ibrahim, ƙaramar ministar harkokin ‘yansanda ta koma ministar mata, Ayodele Olawande, ƙaramin ministan matasa ya koma ministan raya matasa, Dr. Salako Iziaq Adekunle Adeboye, ƙaramin ministan muhalli, ya koma ƙaramin ministan lafiya.

shugaban kasar ya kuma nada sabbin ministocin da suka hadar da Dr Nentawe Yilwatda – Ministan ma’aikatar jinƙai da yaye talauci, Muhamamd Maigari Dingyaɗi – Ministan ƙwadago, Bianca Odinaka Odumegu-Ojukwu – Ƙaramar ministar harkokin waje, Dr Jumoke Oduwale – Ministar ma’aikatar kasuwanci da zuba jari, Idi Mukhtar Maiha – Ma’aikatar kusa da dabbobi, Hon Yusuf Abdullahi Ata – Ƙaramin ministan gidaje da raya birane, Suwaiba Said Ahmad phD – Ministar Ilimi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp