Home General TCN ya magantu kan matsalar rashin wutar lantarki a Arewacin Nijeriya

TCN ya magantu kan matsalar rashin wutar lantarki a Arewacin Nijeriya

Kamfanin samar da lantarki na Najeriya TCN ya ce ya gano abin da ya haifar da matsalar rashin wutar lantarki a wasu yankunan arewacin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da ya fitar, kamfanin ya ce layin samar da lantarki na Ugwuaji-Apir 330-kilovolt ne ya samu matsala.

A ‘yan kwanakin baya-bayan ne wasu yankunan arewacin ƙasar suka fuskanci matsalar katsewar wutar lantarki, lamarin da TCN ya alaƙanta da faɗuwar layin Ugwaji–Apir.

Sanarwar mai ɗauke da sa hannun daraktan hulɗa da jama’a na kamfanin, Ndidi Mbah, ya ce an gano matsalar ne a yankin Igumale na jihar Benue.

Mista Mbah ya ce sai a ranar Laraba ne kamfanin ya gano haƙiƙanin abin da ya faru.

Ya ƙara da cewa tuni kamfanin ya kammala shirye-shiryen tattara kayan aikin da yake buƙata domin fara gyaran layin a wurin da abin ya faru a yau Alhamis.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp