Home General TCN ya magantu kan matsalar rashin wutar lantarki a Arewacin Nijeriya

TCN ya magantu kan matsalar rashin wutar lantarki a Arewacin Nijeriya

Kamfanin samar da lantarki na Najeriya TCN ya ce ya gano abin da ya haifar da matsalar rashin wutar lantarki a wasu yankunan arewacin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da ya fitar, kamfanin ya ce layin samar da lantarki na Ugwuaji-Apir 330-kilovolt ne ya samu matsala.

A ‘yan kwanakin baya-bayan ne wasu yankunan arewacin ƙasar suka fuskanci matsalar katsewar wutar lantarki, lamarin da TCN ya alaƙanta da faɗuwar layin Ugwaji–Apir.

Sanarwar mai ɗauke da sa hannun daraktan hulɗa da jama’a na kamfanin, Ndidi Mbah, ya ce an gano matsalar ne a yankin Igumale na jihar Benue.

Mista Mbah ya ce sai a ranar Laraba ne kamfanin ya gano haƙiƙanin abin da ya faru.

Ya ƙara da cewa tuni kamfanin ya kammala shirye-shiryen tattara kayan aikin da yake buƙata domin fara gyaran layin a wurin da abin ya faru a yau Alhamis.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp