Home General TCN ya magantu kan matsalar rashin wutar lantarki a Arewacin Nijeriya

TCN ya magantu kan matsalar rashin wutar lantarki a Arewacin Nijeriya

Kamfanin samar da lantarki na Najeriya TCN ya ce ya gano abin da ya haifar da matsalar rashin wutar lantarki a wasu yankunan arewacin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da ya fitar, kamfanin ya ce layin samar da lantarki na Ugwuaji-Apir 330-kilovolt ne ya samu matsala.

A ‘yan kwanakin baya-bayan ne wasu yankunan arewacin ƙasar suka fuskanci matsalar katsewar wutar lantarki, lamarin da TCN ya alaƙanta da faɗuwar layin Ugwaji–Apir.

Sanarwar mai ɗauke da sa hannun daraktan hulɗa da jama’a na kamfanin, Ndidi Mbah, ya ce an gano matsalar ne a yankin Igumale na jihar Benue.

Mista Mbah ya ce sai a ranar Laraba ne kamfanin ya gano haƙiƙanin abin da ya faru.

Ya ƙara da cewa tuni kamfanin ya kammala shirye-shiryen tattara kayan aikin da yake buƙata domin fara gyaran layin a wurin da abin ya faru a yau Alhamis.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp