Home Labarai Tinubu ya sallami ministoci biyar cikin kunshin ministocinsa

Tinubu ya sallami ministoci biyar cikin kunshin ministocinsa

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sallami ministoci biyar tare da naɗa wasu sababbi bakwai da kuma sauya wa goma ma’aikatu.

Wata sanarwa da fadar gwamnatin kasar ta fitar a shafinta na X, ta nuna cewa ministocin da aka cire sun hadar da Barr. Uju-Ken Ohanenye; ma’aikatar harkokin mata, Lola Ade-John; ministan harkokin yawon buɗe idanu, Farfesa Tahir Mamman; ministan ilimi, Abdullahi Muhammad Gwarzo; ƙaramin ministan gidaje da raya birane, Dr. Jamila Bio Ibrahim; ministar matasa.

Sai dai shugaba Bola Tinubu ya sauya wasu daga cikin ministocin ma’aikatu da suka hadar da Hon Dr. Yusuf Tanko Sununu; ƙaramin ministan ilimi ya koma ƙaramin ministan jinƙai da rage talauci, Dr. Morufu Olatunji Alausa; ƙaramin ministan lafiya, ya koma ministan ilimi, Barr. Bello Muhammad Goronyo, ƙaramin ministan ruwa da tsafta, ya zama ƙaramin ministan ayyuka, Hon. Abubakar Eshiokpekha Momoh, ministan raya Naija Delta, ya koma ma’aikatar raya yankuna (sabuwa), Uba Maigari Ahmadu, ƙaramin ministan ƙarafa ya koma ƙaramin ministan raya yankuna, Dr. Doris Uzoka-Anite, ministar masana’antu da kasuwanci da zuba jari ta koma ƙaramar ministar kuɗi, Sen. John Owan Enoh, ministan raya wasanni ya koma ƙaramin ministan kasuwanci da zuba jari (masana’antu), Imaan Sulaiman-Ibrahim, ƙaramar ministar harkokin ‘yansanda ta koma ministar mata, Ayodele Olawande, ƙaramin ministan matasa ya koma ministan raya matasa, Dr. Salako Iziaq Adekunle Adeboye, ƙaramin ministan muhalli, ya koma ƙaramin ministan lafiya.

shugaban kasar ya kuma nada sabbin ministocin da suka hadar da Dr Nentawe Yilwatda – Ministan ma’aikatar jinƙai da yaye talauci, Muhamamd Maigari Dingyaɗi – Ministan ƙwadago, Bianca Odinaka Odumegu-Ojukwu – Ƙaramar ministar harkokin waje, Dr Jumoke Oduwale – Ministar ma’aikatar kasuwanci da zuba jari, Idi Mukhtar Maiha – Ma’aikatar kusa da dabbobi, Hon Yusuf Abdullahi Ata – Ƙaramin ministan gidaje da raya birane, Suwaiba Said Ahmad phD – Ministar Ilimi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp