Home Labarai Cire T-Gwarzo Daga Minista Babban Kuskure ne – Kungiya Matasan APC ta...

Cire T-Gwarzo Daga Minista Babban Kuskure ne – Kungiya Matasan APC ta Kasa

Kungiyar matasan jam’iyyar APC ta kasa ta kalubalanci tsige Injiniya Abdullahi Tijjani Gwarzo a matsayin karamin ministan gidaje da raya birane.

Kungiyar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da shugabanta Abdullahi Wada Kura ya sanyawa hannu kuma ta aikowa kadaura24, ta bayyana cire Gwarzo a matsayin abin mamaki da hadari ga jam’iyyar APC a jihar.

“Mafi yawan al’ummar jihar Kano sun tausayawa sakamakon cirewar da aka yi masa. Cire shi daga minista ya haifar da rashin jin dadi kuma zai kawo tsaiko ga tasirin jam’iyyar APC a jihar Kano,” a cewar kungiyar.

T Gwarzo wanda aka tsige shi da wasu mutane 4 ya godewa shugaban kasar da ya bashi damar yiwa kasarsa hidima.

Kungiyar ta yi zargin cewa wani fitaccen dan Siyasa daga jihar kano ne ya kitsa yadda aka cire T Gwarzo daga Minista.

“Wanda ya kitsa cireT Gwarzo ya yaudari shugaban kasa, kuma ya kamata ya sani mutum daya bai isa ya rika yanke shawara da sunan Kano ba,” inji kungiyar

Kungiyar ta yi gargadin cewa wannan mataki kokari ne kawai na karawa jam’iyyar NNPP karfi cikin dubarane, ganin cewa bai kamata a jefar da ’yan siyasa irinsu Gwarzo ba tare da wani kwakkwaran dalili ba.

“Idan ba a mayar da shi Kan mukaminda ba, nan da shekarar 2027, shugaban kasa zai gane ko Gwarzo na jama’a ko ba shi da su, amma ta fito filin cewa al’ummar jihar Kano suna tare da Gwarzo saboda yadda jam’a suka tausaya masa .

“Kano ta Arewa ta zamo babbar shiyyar APC ce saboda yadda Gwarzo da sauran masu ruwa da tsaki suka fito daga shiyyar, ba wai don mutum daya ba.

Ya kamata shugaban kasa ya duba amma matakin da aka dauka shawara ce mai hadari a 2027,”in ji Wanda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp