Home General Jam’iyyun sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya a zaɓen gwamnan Ondo

Jam’iyyun sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya a zaɓen gwamnan Ondo

Jam’iyyun siyasa da ‘yan takara sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a zaɓen gwamnan jihar Ondo da ke kudu maso yammacin Najeriya.

An yi bikin sanya hannun ne ƙarƙashin jagorancin kwamitin zaman lafiya na ƙasa NPC, a cibiyar raya al’adu da ke Akure, babban birni jihar.

Shugaban kwamitin, Janar Abdulsalami Abubakar mai ritaya, ya yi kira ga duka masu ruwa da tsaki su tabbatar an gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali.

Ya kuma buƙaci shugabannin jam’iyyu da ‘yan takara su amince da sakamakon zaɓen matsawar an gudanar da shi cikin kwanciyar hankali da lumana.

A nasa ɓangare shugaban hukumar zaɓen kasar, Farfesa Mahmood Yakubu ya yaba wa kwamitin bisa ƙoƙarinsa na haɗa kan jam’iyyun da ‘yan takara a teburin yarjejeniyar zaman lafiya a lokutan zaɓukan ƙasar.

Farfesa Yakubu ya kuma yi kira ga shugabannin addinai da sarakuna da jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki su haɗa hannu da hukumarsa don gudanar da zaɓen gwamnan jihar cikin kwanciyar hankali da lumana.

A ranar 16 ga watan Nuwamban da muke ciki ne za a gudanar da zaɓen gwamnan jihar ta Ondo.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp